Aminiya:
2025-05-25@16:41:16 GMT

Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci

Published: 16th, March 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana shirin mayar da Filin Idi na Ƙofar Mata zuwa Cibiyar Taro ta Ƙasa da Ƙasa don Harkokin Addinin Musulunci.

Sabuwar cibiyar za ta zama wajen gudanar da taruka da karatuttukan addini maimakon barin filin ana amfani da shi sau biyu a shekara don Sallar Idi.

HOTUNA: NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye a cikin carbi da takalma Akwai ’yan ƙwaya a cikin sarakunan gargajiya — Obasanjo

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin wani taron buɗa-baki da ya shirya a Fadar Gwamnatin jihar a ranar 15 ga watan Ramadan.

Taron ya samu halartar Mambobin Majalisar Malamai, inda suka tattauna kan haɗin kai da kuma rawar da malamai ke takawa wajen wanzar da zaman lafiya.

Gwamna Abba ya ce za a kafa harsashin ginin cibiyar makonni biyu bayan Sallar Idi Ƙarama, sannan daga bisani za a miƙa ta ga malamai don su kula da ita.

Baya ga haka, gwamnan ya kuma bayyana aniyarsa na gyara dukkanin masallatan Juma’a a faɗin jihar don tabbatar da cewa sun zama ingantattun wuraren ibada.

Ya umarci Kwamishinan Harkokin Addini da ya tattara sunayen masallatan da ke buƙatar gyara cikin gaggawa.

Hakazalika, gwamnan ya kuma sanar da cewa ana gina sabon babban Masallacin Juma’a a Fadar Gwamnatin jihar domin ƙara wa masu ibada wajen da ya fi girma da dacewa.

Da yake jawabi a madadin sauran malamai, Sheikh Muhammad Nasir Adam, limamin Masallacin Sheikh Ahmad Tijjani, ya yaba da hangen nesan gwamnan.

Taron ya samu halartar mambobin Hukumar Shari’a, Majalisar Zartarwa, da wasu manyan baƙi.

Gwamnan ya tabbatarwa da malaman addini cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da sauraron shawarwarinsu domin tabbatar da zaman lafiya da daidaito a Kano.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Cibiya Gwamna Abba taro

এছাড়াও পড়ুন:

An Kaddamar Da Babban Filin Wasan Da Kasar Sin Ta Gina Wa Kasar Chadi Kyauta

An kaddamar da wani sabon babban filin wasa a birnin N’Djamena na kasar Chadi, wanda kasar Sin ta gina wa kasar kyauta.

Yayin bikin kaddamarwar da ya gudana ranar Juma’a, shugaban kasar Chadi Mahamat Idriss Deby, ya buga kwallon kafa da kansa, a matsayin alamar fara amfani da babban filin wasan.

Cikin jawabin da ya gabatar, shugaba Deby ya gode wa kasar Sin, gami da bayyana filin wasan a matsayin daya daga cikin sakamakon da aka cimma, bisa huldar hadin kai, da mutunta juna, da ta kasance tsakanin kasashen Chadi da Sin.

Wani kamfanin kasar Sin ne ya gina babban filin wasan tare da mika shi ga kasar Chadi a ranar 12 ga wata. Girman filin wasan ya kai muraba’in mita dubu 33, wanda ya kunshi kujerun masu kallon wasanni dubu 30, da filayen wasan kwallon kafa, da na kwallon kwando, da dimbin na’urorin zamani daban daban. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kaddamar Da Babban Filin Wasan Da Kasar Sin Ta Gina Wa Kasar Chadi Kyauta
  • Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna 
  • Eslami : duk wani mataki da Iran ta dauka ya dogara ne kan manufofi da muradun kasar
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi
  • Arakci Ya Jaddada Muhimmanci Kawo Karshen Yakin Gaza Da Kuma Shigar Da Kayan Agaji
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Kara Haske kan Batun Inganta Sinadarin Uranium Da Zamanta Da Amurka
  • Gwamnan Kano Ya Ceto Dalibai 84 Da Ganduje Yaki Biya Wa Kudin Makaranta A Cyprus
  • SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
  •  Nahiyar Afirka Ta Kafa Cibiyar Tattara Bayanai Akan Yanayi
  • Sojojin Yemen Sun Kai Wa Filin Jirgin Saman “Ben Gorion” Hari Sau Biyu A Yau Alhamis