Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci
Published: 16th, March 2025 GMT
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana shirin mayar da Filin Idi na Ƙofar Mata zuwa Cibiyar Taro ta Ƙasa da Ƙasa don Harkokin Addinin Musulunci.
Sabuwar cibiyar za ta zama wajen gudanar da taruka da karatuttukan addini maimakon barin filin ana amfani da shi sau biyu a shekara don Sallar Idi.
Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin wani taron buɗa-baki da ya shirya a Fadar Gwamnatin jihar a ranar 15 ga watan Ramadan.
Taron ya samu halartar Mambobin Majalisar Malamai, inda suka tattauna kan haɗin kai da kuma rawar da malamai ke takawa wajen wanzar da zaman lafiya.
Gwamna Abba ya ce za a kafa harsashin ginin cibiyar makonni biyu bayan Sallar Idi Ƙarama, sannan daga bisani za a miƙa ta ga malamai don su kula da ita.
Baya ga haka, gwamnan ya kuma bayyana aniyarsa na gyara dukkanin masallatan Juma’a a faɗin jihar don tabbatar da cewa sun zama ingantattun wuraren ibada.
Ya umarci Kwamishinan Harkokin Addini da ya tattara sunayen masallatan da ke buƙatar gyara cikin gaggawa.
Hakazalika, gwamnan ya kuma sanar da cewa ana gina sabon babban Masallacin Juma’a a Fadar Gwamnatin jihar domin ƙara wa masu ibada wajen da ya fi girma da dacewa.
Da yake jawabi a madadin sauran malamai, Sheikh Muhammad Nasir Adam, limamin Masallacin Sheikh Ahmad Tijjani, ya yaba da hangen nesan gwamnan.
Taron ya samu halartar mambobin Hukumar Shari’a, Majalisar Zartarwa, da wasu manyan baƙi.
Gwamnan ya tabbatarwa da malaman addini cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da sauraron shawarwarinsu domin tabbatar da zaman lafiya da daidaito a Kano.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Cibiya Gwamna Abba taro
এছাড়াও পড়ুন:
Matar tsohon Gwamnan Adamawa ta sauya sheka daga PDP zuwa ADC
Matar tsohon Gwamnan jihar Adamawa, Zainab Boni Haruna, ta fice daga tsohuwar jam’iyyarta ta PDP zuwa jam’iyyar hadakar ’yan adawa ta ADC.
Zainab, wacce asalinta ta fito ne daga karamar hukumar Nangere a Jihar Yobe ta bayyana haka ne a wani taro da mata magoya bayan jam’iyyar ta ADC da aka gudanar a Damaturu, babban birnin jihar ta Yobe.
Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikaciyar ofishin jakadancin Ghana a Abuja Kaso 90 na ’yan bindigar da suka addabi Katsina ’yan asalin jihar ne – RaddaZainab Boni ta kuma zargi jam’iyyar APC mai mulki karkashin jagorancin Shugaban Kasa Bola Tinubu kan rashin tsaro, wahalhalu, cin hanci da rashawa da kuma rashin shugabanci na gari a kasar nan.
“Mutane suna shan wahala, yunwa ta yi yawa,” in ji ta.
Ta kara da cewa, “Na yanke shawarar shiga jam’iyyar ADC tare da babban wanda na ke karbar shawara kan harkokin siyasa daga wajen shi, Alhaji Adamu Maina Waziri, wanda na yi imanin cewa yana da karfi da dukiya da kuma manufar siyasa don tunkarar APC a zaben 2027.”
Ta kuma ce da yawa daga ’ya’yan jam’iyyar PDP yanzu haka na ficewa suna komawa ADC saboda ba za a iya sasanta rikicin da ke cikin jam’iyyar ba.
“Kafin na yanke shawarar ficewa daga PDP, sai da na je gidan Adamu Waziri wanda tsohon Ministan Harkokin ’Yan Sanda ne kuma mamba a kwamitin amintattu na PDP domin neman shawarar siyasa a wurinsa, wadda hakan ne ya bani karfin gwiwar yanke wannan shawarar,” in ji ta.
Sai dai ta bukaci mata da matasan sauran jam’iyyun siyasa da su shirya wa babban zaben shekarar 2027.