Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci
Published: 16th, March 2025 GMT
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana shirin mayar da Filin Idi na Ƙofar Mata zuwa Cibiyar Taro ta Ƙasa da Ƙasa don Harkokin Addinin Musulunci.
Sabuwar cibiyar za ta zama wajen gudanar da taruka da karatuttukan addini maimakon barin filin ana amfani da shi sau biyu a shekara don Sallar Idi.
Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin wani taron buɗa-baki da ya shirya a Fadar Gwamnatin jihar a ranar 15 ga watan Ramadan.
Taron ya samu halartar Mambobin Majalisar Malamai, inda suka tattauna kan haɗin kai da kuma rawar da malamai ke takawa wajen wanzar da zaman lafiya.
Gwamna Abba ya ce za a kafa harsashin ginin cibiyar makonni biyu bayan Sallar Idi Ƙarama, sannan daga bisani za a miƙa ta ga malamai don su kula da ita.
Baya ga haka, gwamnan ya kuma bayyana aniyarsa na gyara dukkanin masallatan Juma’a a faɗin jihar don tabbatar da cewa sun zama ingantattun wuraren ibada.
Ya umarci Kwamishinan Harkokin Addini da ya tattara sunayen masallatan da ke buƙatar gyara cikin gaggawa.
Hakazalika, gwamnan ya kuma sanar da cewa ana gina sabon babban Masallacin Juma’a a Fadar Gwamnatin jihar domin ƙara wa masu ibada wajen da ya fi girma da dacewa.
Da yake jawabi a madadin sauran malamai, Sheikh Muhammad Nasir Adam, limamin Masallacin Sheikh Ahmad Tijjani, ya yaba da hangen nesan gwamnan.
Taron ya samu halartar mambobin Hukumar Shari’a, Majalisar Zartarwa, da wasu manyan baƙi.
Gwamnan ya tabbatarwa da malaman addini cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da sauraron shawarwarinsu domin tabbatar da zaman lafiya da daidaito a Kano.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Cibiya Gwamna Abba taro
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Za Ta Yi Nazarin Sabuwar Gayyatar Da Amurka Ta Yi Mata Na Sabuwar Tattaunawa
Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta sanar da cewa, tana nazarin sabuwar gayyatar da Amurka ta yi mana na komawa teburin tattaunawa.
Kamfanin dillancin labarun “Mehr” na Iran ya nakalto wata majiya mai karfi tana cewa, bayan da Amurka ta kasa dakatar da Shirin kasar na makamashin Nukiliya, ta aiko ma ta da takardar gayyata domin yin zama da ita akan teburin tattaunawa.
Majiyar ma’aikatar harkokin wajen Iran ta fada wa kamfanin dillancin labrun “Mehr” cewa, Amurka ta aiko da sakwanni ta hanyar ‘yan aike na kasashe masu yawa.”
Ma’aikatar harkokin wajen ta Jamhuriyar musulunci ta Iran tana yin nazari akan hakikanin abinda Amurkan take so, da kuma yadda tattaunawar za ta kasance wacce za ta zama ta dage takunkumai, da kuma darajar uranium din da Iran za ta tace, sannan kuma da biyanta… na barnar da aka yi mata sanadiyyar kallafaffen yaki.
Tun da dari, Amurka ta yi kokarin nuna cewa Iran ce ta bukaci ayi tatttaunawar, lamarin da Jamhuriyar musulunci ta Iran ta kore.
Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Akarci, ya sha bayyana cewa, duk wata tattaunawa idan har za a yi ta, to za ya kasance ne akan manufar kare maslahar jamhuriyar musulunci ta Iran. Batun ci gaba da tace nadarin uranium kuwa, wani abu wanda Iran ba za ta taba ja da baya a kansa ba.