Tattalin Arzikin Ghana Ya Bunkasa Da Kashi 5.7 A Shekarar 2024
Published: 16th, March 2025 GMT
Hukumar kididdiga ta kasar Ghana ta ce, tattalin arzikin Ghana ya bunkasa da kashi 5.7 cikin 100 a shekarar 2024, sakamakon gagarumin aikin masana’antu, a daidai lokacin da ake gudanar da sauye-sauyen tattalin arzikin kasar da asusun ba da lamuni na duniya (IMF) ke marawa baya.
Da yake jawabi ga manema labarai jiya litinin a Accra, babban birnin Ghana, Babban jami’in kididdiga na gwamnatin kasar, Samuel Kobina Annim, ya ce bunkasar tattalin arzikin ya kai kashi 2.
Ya kara da cewa, “Duk da an samu tafiyar hawainiya a karuwar kashi 0.2 cikin 100 a rubu’i na hudu, bangaren masana’antu ya jagoranci ci gaban tattalin arzikin Ghana a shekarar 2024 tare da samun karuwar kashi 7.1 cikin 100, sakamakon ayyukan gine-gine da ma’adinai da fasa duwatsu.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: tattalin arzikin
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a yi koyi daga akidun dan mazan jiya, kuma jagora na gari Chen Yun, tare da kara azamar dorar da kyawawan dabi’unsa cikin himma da kwazo, don gina kasar Sin mai matukar karfi.
Shugaba Xi, wanda shi ne babban sakataren kwamitin kolin JKS, kana shugaban hukumar koli ta rundunar sojojin kasar, ya yi kiran ne a yau Juma’a, cikin jawabin da ya gabatar, yayin taron bikin murnar cika shekaru 120 da haihuwar Chen Yun, taron da ya gudana a babban dakin taruwar jama’a dake tsakiyar birnin Beijing
Shugaban na Sin ya ce, an haifi Chen a shekarar 1905, ya kuma shiga JKS a shekarar 1925. Ya kuma kasance shahararren dan gwagwarmaya a rundunar ‘yantar da al’umma kuma dattijon arziki, kana daya daga cikin kusoshin da suka kafa tsarin tattalin arziki na gurguzu na kasar Sin. Kazalika, ya kasance muhimmin memba cikin jerin shugabannin JKS zangon farko mai Mao Zedong a matsayin babban jigo, kana da shugabannin JKS zango na biyu mai Deng Xiaoping a matsayin babban jigo. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp