Kalmar demokuradiyya kalma ce da jagoran ‘yan awaren Taiwan Lai Ching-te ke yawan ambata, amma aikin da ya yi bai bi hanyar demokuradiyya ba. A baya-bayan nan, Lai Ching-te ya gabatar da wani shirin neman ‘yancin kan Taiwan, har ma ya ce wai Taiwan wata kasar demokuradiyya ce mai mulkin kanta. Lai Ching-te ya kan yin amfani da demokuradiyya don ya cuci jama’ar yankin Taiwan da sauran kasashen duniya, amma a wannan karo kowa ya san yunkurinsa na neman mulki irin na kama karya ta hanyar demokuradiyya.

Ya kamata a yi amfani da demokuradiyya don tabbatar da hakkin jama’a, a maimakon kawo illa ga hakkin jama’a. Jama’ar yankin Taiwan suna neman zaman lafiya, da samun ci gaba, da yin mu’amala, da kuma yin hadin gwiwa. Bisa binciken shekara kan huldar dake tsakanin bangarori biyu na mashigin tekun Taiwan da kafofin watsa labaru na yankin Taiwan suka bayar a shekarar 2024, kashi 87 cikin dari na jama’ar yankin Taiwan sun yi tsammanin cewa, akwai bukatar kiyaye yin mu’amala a tsakanin bangarorin biyu na mashigin tekun Taiwan. Amma tun lokacin da mahukuntan jagoran ‘yan awaren Taiwan Lai Ching-te suka kama aiki a watan Mayu na shekarar bara, sun yi amfani da hanyoyin ayyukan gwamnati da dokoki da kafofin watsa labaru don hana yin mu’amala a tsakanin bangarorin biyu na mashigin tekun Taiwan.

Mahukuntan Lai Ching-te sun yi aika-aikar da ta janyo koma baya a tarihi da keta ‘yanci da hakkin dan Adam na jama’ar yankin Taiwan, kana tana son shigar da jama’ar cikin ayyukan ‘yan awaren Taiwan, da bayyana cewa wai yankin Taiwan muhimmin yanki ne da ke tabbatar da demokuradiyya a duniya. Yunkurinsa na neman ‘yancin kan Taiwan wanda ya keta bukatun jama’a da demokuradiyya ba zai samu nasara a tarihi ba. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: jama ar yankin Taiwan a ar yankin Taiwan da demokuradiyya

এছাড়াও পড়ুন:

Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno

Sanata Ali Ndume, mai wakiltar yankin Borno ta Kudu, ya bayyana cewa hare-haren na ƙara ƙamari a yankin abun takaici ne.

Ya ce ya samu rahoto tsakanin Hawul da Garkida inda aka ce an kashe ’yan sa-kai sama da 10 a ranar Litinin.

A cewarsa, sama da mutane 100 aka kashe cikin wata guda a hare-hare da aka kai Sabon Gari, Izge, Kirawa, Pulka, Damboa, Chibok, Askira Uba da wasu garuruwa da dama.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • Wang Yi: Neman Sulhu Da Ja Da Baya Riba Ne Ga Masu Son Cin Zali
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano
  • NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”
  • An kashe sojoji 12 a barikin Nijar