Aminiya:
2025-12-09@10:18:40 GMT

Sojoji sun kashe ’yan bindiga 31, sun lalata sansaninsu a Katsina

Published: 16th, March 2025 GMT

Dakarun Sojin Najeriya sun kashe ’yan bindiga 31 tare da lalata sansaninsu a Jihar Katsina, yayin wasu hare-hare guda biyu da suka kai.

A farmaki na farko, dakarun Operation Fansan Yamma sun yi artabu da ’yan bindiga a garin Maigora da ke Ƙaramar Hukumar Faskari.

Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga Amurka

Da farko, sojojin sun kashe ’yan bindiga biyar bayan sun kai farmaki garin.

Sai dai lokacin da suka sake haɗuwa don kai harin ramuwar gayya, sojojin sun sake kashe guda bakwai, ciki har da Dogo, wanda babban Kwamanda ne a cikinsu.

Haka kuma, sojojin sun ƙwace babura guda bakwai da ‘yan bindigar ke amfani da su.

A wani farmakin, rundunar sojojin sama ta yi luguden wuta a maboyar ’yan bindiga da ke dajin Unguwar Goga, Ruwan Godiya, a Ƙaramar Hukumar Faskari.

Sun lalata sansanin shugabannin ’yan bindiga biyu; Alhaji Gero da Alhaji Riga, inda suka kashe aƙalla mahara 19.

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa sojojin Najeriya na ƙara ƙaimi wajen murƙushe ’yan bindiga a yankin Arewa maso Yamma, tare da lalata sansaninsu.

Har ila yau, sojojin na ci gaba da sintiri ta sama da ƙasa don daƙile yunƙurin ’yan bindiga na sake hare-hare.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga dakaru hare hare yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda

Daga Isma’il Adamu

Jam’iyyar NNPP ta bayyana cewa tana da kwarin gwiwar lashe karin mukaman siyasa a zaben shekarar 2027, ciki har da na shugaba kasa da gwamnan Jihar Katsina.

Sabon shugaban jam’iyyar da aka rantsar a Jihar Katsina, Alhaji Armaya’u AbdulKadir ne ya bayyana haka a zaben shugabannin jam’iyyar da aka gudanar a Katsina.

Ya ce jam’iyyar, wacce ta ba da muhimmanci ga ilimi, walwalar jama’a, karfafa matasa da ci gaban abubuwan more rayuwa, ta kara samun farin jini a wajen jama’a saboda ingantaccen jagoranci da wakilcin da take bayarwa ta hannun mambobinta da ke rike da  mukamai a matakin kananan hukumomi, jihohi da tarayya.

“Masu zabe sun ga abin da jam’iyyarmu ke aiwatarwa. ‘Yan majalisa da sauran wadanda aka zaba suna aiki a matakai daban-daban tun daga kananan hukumomi har zuwa matakin tarayya. ‘Yan Najeriya sun shaida kwarjininmu, shi ya sa muke da tabbacin lashe karin kujeru a zaben 2027.

“Jagoranmu na kasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya kuduri aniyar karbar shugabancin kasa, yayin da a nan Jihar Katsina kuma muke shirin tsayar da kwararru masu kwarewa da kuzari da za su iya lashe kujerar Gwamna da sauran mukaman zabe.”

AbdulKadir, wanda ya jaddada cewa NNPP na kara samun karbuwa a tsakanin ‘yan Najeriya, ya ce hakan ya nuna a kwanan nan ta hanyar sauya sheka da wasu ‘yan wasu jam’iyyu suka yi zuwa NNPP. Ya kuma bukaci mambobin jam’iyyar da su kara samun magoya baya domin tunkarar zaben 2027.

Zaben shugabannin jihar, wanda ya samar da mambobi 38 ta hanyar maslaha, ya samu kulawar INEC da hukumomin tsaro, tare da halartar wakilan jam’iyyar daga kasa da yankin Arewa maso Yamma, da kuma daruruwan mambobin jam’iyyar.

Alhaji Armaya’u AbdulKadir ya  kasance Shugaban jam’iyya, Sani Arga mataimaki na farko, Tijjani Zakari sakatare, Umar Musa sakataren shirya ayyuka, sannan Hauwa Abubakar ta zama shugabar mata.

Tunda farko, shugaban kwamitin gudanar da taron, Alhaji Muhammad Yusuf-Fagge, ya yaba wa wakilai da mambobin jam’iyyar a jihar bisa ladabi da natsuwar da suka nuna a yayin taron, da kuma yadda suka amince da hanyar maslaha wacce “ta sauƙaƙa aikin.”

Ya yi kira ga mambobin jam’iyyar a jihar da su ci gaba da kasancewa cikin hadin kai, biyayya da ladabi, tare da kara yawaita mambobi da samun goyon baya ga jam’iyyar a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a Sakkwato
  • Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
  • ’Yan bindiga ya hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
  • Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Jamhuriyar Benin
  • Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan
  • ’Yan bindiga sun harbe ɗan sanda har lahira a Edo
  • Shugaban Majalisar Dattawan Akpabio ya Nemi Sanata Natasha ta Biya Shi Diyyar Biliyan 200