Sojoji sun kashe ’yan bindiga 31, sun lalata sansaninsu a Katsina
Published: 16th, March 2025 GMT
Dakarun Sojin Najeriya sun kashe ’yan bindiga 31 tare da lalata sansaninsu a Jihar Katsina, yayin wasu hare-hare guda biyu da suka kai.
A farmaki na farko, dakarun Operation Fansan Yamma sun yi artabu da ’yan bindiga a garin Maigora da ke Ƙaramar Hukumar Faskari.
Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga AmurkaDa farko, sojojin sun kashe ’yan bindiga biyar bayan sun kai farmaki garin.
Sai dai lokacin da suka sake haɗuwa don kai harin ramuwar gayya, sojojin sun sake kashe guda bakwai, ciki har da Dogo, wanda babban Kwamanda ne a cikinsu.
Haka kuma, sojojin sun ƙwace babura guda bakwai da ‘yan bindigar ke amfani da su.
A wani farmakin, rundunar sojojin sama ta yi luguden wuta a maboyar ’yan bindiga da ke dajin Unguwar Goga, Ruwan Godiya, a Ƙaramar Hukumar Faskari.
Sun lalata sansanin shugabannin ’yan bindiga biyu; Alhaji Gero da Alhaji Riga, inda suka kashe aƙalla mahara 19.
Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa sojojin Najeriya na ƙara ƙaimi wajen murƙushe ’yan bindiga a yankin Arewa maso Yamma, tare da lalata sansaninsu.
Har ila yau, sojojin na ci gaba da sintiri ta sama da ƙasa don daƙile yunƙurin ’yan bindiga na sake hare-hare.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga dakaru hare hare yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamandan Sojojin Iran Ya Ziyarci Gidan Babban Jami’in Sojin Kasar Da Ya Yii Shahada Lokacin Yakin Baya-Bayan Nan
Kwamandan sojojin kasar Iran ya jaddada cewa: Sojojin Iran sun shirya tsaf don kare juyin juya halin Musulunci da kasarsu
A yayin ziyarar da ya kai wa iyalan shahidi kwamandan tsaron cikin gida na kasar Iran Kanal Mohammad Alizadeh; Babban kwamandan sojojin kasar Iran Manjo Janar Amir Hatami ya bayyana cewa: Jajirtattun sojojin kasar Iran a shirye suke da dukkanin karfinsu wajen kare kyawawan manufofin juyin juya halin Musulunci da kuma dukkanin yankin Jamhuriyar Musulunci ta Iran a cikin kowane irin yanayi da kuma fuskantar duk wani mai neman wuce gona da iri.
Manjo Janar Amir Hatami, babban kwamandan sojojin kasar Iran, tare da rakiyar Hujjatul-Islam Ahmad Jalili Safat, mataimakin shugaban bangaren rukunan siyasa ta sojojin kasar, Manjo Janar Muhammad Yousufi Khosh-Qalb, mataimakin kodinetan sojojin sama, da Hujjatul-Islam Muhammad Bahman, shugaban sashen siyasa na bangaren sojan sama, Muhammad Ali sun ziyarci gidan shahidi jajirceccen mayakin rundunar sojin saman Iran kanal Muhammad Ali Zadeh, inda suka gana da iyalan wannan shahidi mai girma tare da girmama matsayin daukakarsa na samu shahada.
A yayin wannan ziyarar, Manjo Janar Hatami ya mika sakon taya murnar shahadar narigayi da ta’aziyyar tashinsa, gami da tunawa da wannan shahidi daga rundunar sojojin sama da dukkan sauran shahidai masoya masu girma da suka sadaukar da kansu a lokacin wuce gona da irin da yahudawan sahayoniyya suka kawo hare-haren ta’addanci kan Iran. Yana mai jaddada cewa: Shahadan bayin Allah salihai a cikin wannan harin wuce gona da iri, ya nuna girman ta’addancin makiya masu dauke da ruhin zalunci, kuma lallai sun tarar da jajirtattun gwarazan Iraniyawa da suka sadaukar da kansu domin kare al’umma da kasarsu.