Sojoji sun kashe ’yan bindiga 31, sun lalata sansaninsu a Katsina
Published: 16th, March 2025 GMT
Dakarun Sojin Najeriya sun kashe ’yan bindiga 31 tare da lalata sansaninsu a Jihar Katsina, yayin wasu hare-hare guda biyu da suka kai.
A farmaki na farko, dakarun Operation Fansan Yamma sun yi artabu da ’yan bindiga a garin Maigora da ke Ƙaramar Hukumar Faskari.
Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga AmurkaDa farko, sojojin sun kashe ’yan bindiga biyar bayan sun kai farmaki garin.
Sai dai lokacin da suka sake haɗuwa don kai harin ramuwar gayya, sojojin sun sake kashe guda bakwai, ciki har da Dogo, wanda babban Kwamanda ne a cikinsu.
Haka kuma, sojojin sun ƙwace babura guda bakwai da ‘yan bindigar ke amfani da su.
A wani farmakin, rundunar sojojin sama ta yi luguden wuta a maboyar ’yan bindiga da ke dajin Unguwar Goga, Ruwan Godiya, a Ƙaramar Hukumar Faskari.
Sun lalata sansanin shugabannin ’yan bindiga biyu; Alhaji Gero da Alhaji Riga, inda suka kashe aƙalla mahara 19.
Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa sojojin Najeriya na ƙara ƙaimi wajen murƙushe ’yan bindiga a yankin Arewa maso Yamma, tare da lalata sansaninsu.
Har ila yau, sojojin na ci gaba da sintiri ta sama da ƙasa don daƙile yunƙurin ’yan bindiga na sake hare-hare.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga dakaru hare hare yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya sake naɗa Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA
Shugaba Kasa Bola Ahmed Tinubu ya sake nada Birgediya-Janar Mohammed Buba Marwa (mai ritaya) a matsayin Shugaban Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA) na tsawon shekaru biyar masu zuwa.
Bayo Onanuga, Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labaru, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a ranar Juma’a.
An kama ’yan Najeriya 3 a Kenya kan zargin aikata damfara Majalisar Wakilai ta dage lokacin fara yin jarabawar WAEC a kwamfuta zuwa 2030An fara nada Marwa a watan Janairu 2021 ta hannun
Marigayi Shugaba Muhammadu Buhari ne ya fara naɗa Buba Marwa a muƙamin a watan Janairun 2021, bayan ya jagoranci Kwamitin Shugaban Kasa na Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi daga shekarar 2018 zuwa Disamba 2020.
Sabon nadin na nufin tsohon hafsan soja dan asalin jihar Adamawa zai ci gaba da rike mukamin har zuwa shekarar 2031.
Marwa, wanda ya taba zama gwamnan soja na jihohin Legas da Borno, ya kammala karatu a Makarantar Soja ta Najeriya da kuma Kwalejin Tsaro ta Najeriya (NDA).
Bayan ya zama cikakken soja a shekarar 1973, Marwa ya yi aiki a matsayin babban jami’in 23 Armoured Brigade, ya kasance babban dogari ga tsohon Babban Hafsan Soja, Laftanar-Janar Theophilus Danjuma, sannan ya yi aiki a matsayin Magatakardar Kwalejin Tsaro ta Najeriya.
Haka kuma ya yi aiki a matsayin Mataimakin Mashawarci kan Tsaro a Ofishin Jakadancin Najeriya da ke Washington DC, daga baya kuma ya zama Mashawarci kan Tsaro a Ofishin Jakadan Najeriya na Dindindin a Majalisar Dinkin Duniya.
Zaman Marwa a NDLEA ya yi fice wajen kama masu fataucin miyagun kwayoyi, inda aka cafke sama da mutane 73,000 da ke harkar fatauci da kuma kwace fiye da tan miliyan 15 na miyagun kwayoyi iri-iri.
A karkashin jagorancinsa, hukumar ta kaddamar da gangamin yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a faɗin Najeriya.
Shugaba Tinubu ya ce: “Sake nadinka alamar amincewa ce da kokarinka na kawar da kasar nan daga annobar fatauci da shan miyagun kwayoyi. Ina rokonka kada ka yi kasa a gwiwa wajen bin diddigin ’yan kasuwar miyagun kwayoyi da ke neman lalata al’ummarmu, musamman matasa.”