Leadership News Hausa:
2025-10-20@11:39:14 GMT

Ma’aikatar Ilimin Amurka Na Shirin Korar Ma’aikata 1,300

Published: 16th, March 2025 GMT

Ma’aikatar Ilimin Amurka Na Shirin Korar Ma’aikata 1,300

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Gombe ya ƙaddamar da shirin tallafa wa karatun yara mata

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ƙaddamar da shirin AGILE na tallafin karatun yara mata da tallafin gyaran makarantu, domin inganta ilimi a faɗin jihar.

A wajen bikin da aka gudanar a Otal ɗin Custodian, Gwamna Inuwa, wanda Mataimakinsa Dakta Manasseh Jatau, ya wakilta, ya ce gwamnati na da niyyar kawar da duk wani abin da ke hana yara mata zuwa makaranta.

’Yan sanda sun ƙwato miyagun ƙwayoyi a Gombe Ba mu ji dadin yi wa mahaifinmu afuwa tare da riƙaƙƙun masu laifi ba – Iyalan Herbert Macaulay

Ya ƙara da cewa: “Idan ka ilmantar da ’ya mace, ka ilmantar da al’umma gaba ɗaya; idan ka karfafe ta, ka karfafu zuri’a baki ɗaya.”

Gwamnan, ya gode wa Bankin Duniya, Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, da Kwamitin AGILE saboda haɗin kansu wajen inganta ilimi a jihar.

Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki tare da su domin ɗorewar shirin.

Kwamishiniyar Ilimi ta Jihar Gombe, Dokta Aishatu Umar Maigari, ta ce wannan shiri babban ci gaba ne wajen inganta makarantu da bunƙasa tsarin kula da su ta hannun SBMCs.

Ta buƙaci masu ruwa da tsaki su tabbatar da cewa an yi amfani da kuɗaɗen tallafin yadda ya kamata.

A nata ɓangaren, Kodinetar Shirin AGILE, Dokta Amina Haruna Abdul, ta ce dubban yara mata za su amfana da tallafin domin rage matsin tattalin arziƙi da ke hana su karatu.

Ta kuma yaba da jajircewar gwamnatin jihar, wajen tallafa wa ilimi, inda ta ce hakan zai ƙara wa yara mata ƙwarin gwiwa su ci gaba da neman ilimi a faɗin jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin HKI Sun Shiga Cikin Yankin Qunaidhara Na Kasar Syria
  • ’Yan sanda sun tsare ɗan jarida kan zargin ɓata sunan hadimin gwamnan Kano
  • Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
  • Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103
  • Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano
  • Iran: Kauyuka Guda Uku Na Kasar Sun Shiga Cikin Kauyukan Yawon Shakatawa Ta Duniya
  • Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO
  • Gwamnan Gombe ya ƙaddamar da shirin tallafa wa karatun yara mata
  • Ma’aikatar Kasuwanci Ta Kasar Sin: Sin Za Ta Kyautata Matakan Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth
  • 2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara