Jagoran juyin juya halin musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamnei wanda yake mayarwa da Amurka martani ya bayyana cewa: Ya kamata su daina yin Magana maras ma’ana, fadin cewa Iran ba ta da izinin tace sanadarin Uranium, ganganci ne,domin jamhuriyar musulunci ba ta da bukatar izinin wani mahaluki.

 Jagoran juyin musuluncin na Iran wanda ya gana da iyalan shahid Ra’isi da sauran shahidan hidima, da safiyar yau Talata, ya kara da cewa: Manufar girmama shahidai da kuma jinjinawa ayyukan da su ka yi, shi ne daukar darussa daga rayuwarsu.

Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya kuma ce; Abinda ake fada dangane da shahid Ra’isi shi ne cewa ya kasance mai dukkanin siffofin jami’in da yake wakiltar hukumar da ta ginu akan bin tsarin Allah, wanda ya kasance ya yi aiki tukuru ba tare da gajiyawa ba.” Haka nan kuma jagoran ya bayyana shugaban kasar ta Iran da ya yi shahada da cewa, mutum ne wanda ya kasance mai hidima ga al’umma da daukaka matsayinta, wanda hakan wani darasi ne mai girma na samari da matasa da zuriyar da za ta zo a nan gaba.

 Haka nan kuma Ayatullah Sayid Ali Khamnei ya yi ishara da tattaunawar da ake yi da Amurka ta hanyar shiga Tsakani, yana mai kara da cewa; Abinda Amurka ta furta cewa ba za ta bai wa  Iran damar tace sanadarin uranium ba, ganganci ne,domin jamhuriyar musulunci za ta gaba da tafiyar akan tafarkin da take kansa.”

Jagoran na juyin musulunci ya ce, a nan gaba za yi wa al’umma bayani akan manufar da ta sa suke bijiro da wannan Magana da nanatawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35

Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta zama kasa ta farko a duniya da ta harbo jiragen saman yaki kirar F-35

Iran ta zama kasa ta farko a duniya da ta yi nasarar harbo jiragen yaki kirar F-35, bayan da ta yi nasarar auna wasu jiragen saman yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila kirar F-35 guda biyu, kuma ta barar da su kasa.

Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta yi amfani da wadannan jirage masu tsananin ci gaban zamani wajen kai hare-haren wuce gona gona da iri kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran da safiyar ranar Juma’a, wanda hare-haren suka yi sanadiyyar shahadar wasu manyan jami’an sojan Iran da masana kimiyyar nukiliya da fararen hula da suka hada da mata da kananan yara.

Ma’aikatar hulda da jama’a ta rundunar sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta sanar a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa: Dakarun tsaron saman Iran sun harbo jiragen saman yaki kirar F-35 guda biyu, baya ga wasu jiragen saman yakin yahudawan sahayoniyya marasa matuka ciki.

Sanarwar ta nuna cewa: Jami’an tsaron Iran sun kame daya daga cikin matukan jiragen wacce mace ce, kuma ana kan bincike domin sanin makomar matukin daya jirgin.

Abin lura shi ne cewa: Jiragen yakin kirar F-35 da ‘yan sahayoniyya ke amfani da su na daga cikin wadanda suka ci gaba a duniya kuma ake gwada su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Aike Da Sako Ga Al’ummar Iran Bayan Harin Da Iran Ta Fuskanta
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  •  Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri
  • Jagora Ya Bambance Tsakanin Majalisun Dokokin Kasashe A Fagen Gudanar Da Ayyukan Kasa
  • Iran Ta Ce: Rashin Dakatar Da Uranium Da Dage Takunkumi Sune Hanyar Warware Takaddamar Da Ita