Zaɓen 2027: An soma liƙa fastocin takarar shugaban ƙasa na Gwamnan Bauchi
Published: 22nd, April 2025 GMT
A ranar Litinin ɗin nan aka wayi gari da fastocin takarar shugaban ƙasa a Zaɓen 2027 na Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed.
An liƙa fastocin wuri-wuri da suka haɗa da shataletale da turakun wutar lantarki da allunan tallace-tallace daban-daban a wasu manyan tituna da ke ƙwaryar birnin na Bauchi.
Aminiya ta ruwaito cewa fastocin masu ɗauke da saƙon “Kaura for President” an manna su a wasu manyan hanyoyi da suka haɗa da titin jirgin ƙasa, Sabon Titin Karofi da kuma Ƙofar Dumi.
Ɗaya daga cikin matasan da ke aikin manna fastocin, Aminu Auwal, ya shaida wa Aminiya cewa wasu ’yan siyasa biyu — Ya’u Ortega da Talolo — ne suka ba su kwangilar.
Auwal ya ce: “an ba mu kwangilar liƙa fastocin gwamnan a manyan hanyoyi da ke cikin birnin Bauchi.
“Tun wurin ƙarfe 1:00 na dare muka fara wannan aiki kuma muna sa ran kammalawa a yau [Litinin].”
Sai dai ƙoƙarin jin ta bakin ’yan siyasar biyu da suka ba da wannan kwangilar ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Bauchi Kauran Bauchi takarar shugaban ƙasa
এছাড়াও পড়ুন:
Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi watsi da zargin cewa gwamnatinsa na ƙoƙarin mayar da Nijeriya kan tsarin ƙasa da ke kan tafarkin jam’iyya ɗaya a ƙarƙashin mulkinsa.
Shugaban ya kore wannan zargin ne a yayin jawabin da ya yi na zagayowar Ranar Dimokuraɗiyya a zauren majalisar dokokin ƙasar da ke Abuja, yau Alhamis.
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwaman Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyyaTinubu ya ce masu tunanin cewa APC na son mayar da Nijeriya ƙasa mai jam’iyya ɗaya, to tunanin nasu kuskure ne, kuma suna yin sa cikin ruɗani ne.
Ya ce: “Tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu. Kuma ba zai taɓa zama cikin manufofinmu ba.”
Sai dai shugaban ya ce wannan ba zai hana jam’iyyar APC yin maraba da duk wanda ke son shiga cikinta ba.
“Zai kasance mun yi maguɗin siyasa idan muka hana mutane daga wasu jam’iyyun siyasa shigowa jam’iyyar APC,” in ji Tinubu.
Sai dai Tinubun ya ce suna farin cikin da rikicin ci gida da ke addabar jam’iyyun adawa kuma ba zai shawarar yadda za su warware matsalolinsu ba.
“Ina jin daɗin ganin jam’iyyun adawa a cikin ruɗani, saboda hakan nasara ce bangarenmu.
“Najeriya ba za ta zama ƙasa mai jam’iyya ɗaya ba, batun jam’iyya ɗaya bai ta taso ba, amma siyasar za ta taɓarɓare idan muka rufe ƙofa ga masu son shiga APC,” in ji shi.