Aminiya:
2025-04-30@20:39:03 GMT

A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi

Published: 13th, April 2025 GMT

Sakamakon gazawar shugabanci, bayar da tallafi na neman zama wani bangare a tarihin dimokoradiyyar Nijeriya, inda gwamnatocin jihohi da ’yan majalisu da sauran ’yan siyasa suke amfani da shi wajen cusa wa ’yan kasa ra’ayinsu na siyasa.

A duk lokacin da al’umma suka koka a kan wani mummunann yanayi da ya hada da matsin tattalin arziki da gobarar tankar mota da ambaliyar ruwa da gobara, abin da yake biyo baya shi ne gwamnati ta raba tallafin shinkafa da sauaran kayan abinci, tamkar shinkafa ita ce maganin duk wata matsala.

A wasu lokutan, a kan raba babura masu kafa uku da dabbobi a matsayin tallafi.

Makudan kudaden da gwamnatoci suke kashewa da sunan bayar da tallafi, inda ba a ganin tasirin hakan a rayuwar ’yan kasa, lamari ne da ke ci gaba da damun ’yan Nijeriya. Alal misali, makudan kudaden da gwamnatocin jihohi arewa suka ware da sunan ciyarwar watan Ramadana ya saha suka daga ’yan kasar da dama, cikinsu har da masu amfana da ciyarwar.

A yayin da Gwamnatin Jigawa ta sanar da kashe Naira biliyan 4.8, ita kuwa Gwamnatin Kano ta ware Naira biliyan 8 domin ciyarwar Ramadanan 2025. Gwamnatin Sakkwato ta ware Naira biliyan 6.7, yayin da Gwamnatin Kebbi ta ware Naira biliyan 1.5, inda Gwamnatin Neja ta ware Naira miliyan 976. A nata bangaren, Gwamnatin Yobe ta ware Naira miliyan 298. Uwa-uba, Gwamnatin Katsina ta ware Naira biliyan 10 duk don ciyarwar watan Ramadana.

Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa

Damuwar da masu ruwa da tsaki suka bayyana ita ce yadda gwamnatocin suka kashe wadannan makudan kudade da sunan shirin ciyarwar Ramadana. Misali, shirin ciyarwar Gwamnatin Jigawa an yi hadin gwiwa ne tsakanin gwamnatin jihar da kananan hukumomi bisa kaso 55 da 45. Rashin tabbacin da ke tattare da wannan shiri shi ne su wane ne ainihin wadanda suka amfana da wannan shiri na ciyarwa, sannan kuma wanne tsari aka bi wajen rabo?

A wata ziyar ba-zata da Gwaman Jihar Jigawa ya kai daya daga wuraren ciyarwar a karamar Hukumar Dutse a Ramadanan da ya gabata, ya nuna rashin gamsuwarsa dangane da tsarin da ya gani, wanda hakan ya tabbatar da sukar da al’umma suke yi a kan rashin tsarin shirin ciyarwar. Gwamna Namadi ya nuna rashin amincewarsa game da rashin tsari da karancin abincin a cibiyoyi 609 da aka tsara za su bayar da abinci kala uku ga masu rauni da talakawa 182,700 a kullum. Ya koka da cewa, ‘‘Ban gamsu ba, kodayake ban yi mamaki ba da rashin tsari da sakacin da na gani ba a yau. Ba zai yiwu ba wasu ’yan tsiraru su hana mutanenmu amfana da abin da suka cancanci su samu ba.’’

Duba da irin yadda aka tafiyar da shirin ciyarwar Ramadana, shirin cike yake da almubazaranci da kudin al’umma. Rashin tartibiyar hanyar tabbatar da wadanda suka amfana da shirin, ita ce ta ba wa cin-hancin kofar shigowa. Wannan wata sabuwar hanyar satar kudin al’umma ce cikin sauki da sunan bayar da tallafi, da ya kunshi ciyar da masu rauni a watan Ramadana.

A yayin da ba za a sa kafa a shure irin rawar da bayar da tallafin gwamnati yake takawa ba a yanayi na gaggawa, masu rauni da talakawa za su fi amfana, idan aka saka wadannan makudan kudade a harkar noma da samar da aikin yi ga matasa da mata da samar da kanan masana’antu, wadanda za su samar da mafita ta dindindin. Gwamnati ta yi wa bayar da tallafi mummunar fahimta, duba da yadda ta ba shi muhimmanci, wanda hakan ke nuna dalilin da ya sa aka kasa warware matsalolin kasa yadda ya kamata.

Ya kamata bayar da tallafi ya zamto saboda wasu dalilai na musamman, da nufin bayar da agaji na wucin-gadi, ba samar da mafita ta dindindin ba ga muhimman matsalolin kasa kamar talauci da rashin aikin yi ba. Ana bayar da tallafi ne ga mutanen da suke cikin yaki kamar a yankin Sudan da Gaza.

Shugabanni, musamman gwamnonin jihohi sun fi fifita raba tallafi a al’amuansu na gwamnati, ta yadda kusan ya zama wata hanya ta kimanta ayyukan zababbun masu rike da mukaman gwamnati, duk dai saboda sun gaza fahimtar yadda ake kimanta matsayin tattalin arzikin mutane, wanda ya hada da talauci da tallafi.

Ware makudan kudade domin ciyarwar watan Ramadana ba ita ce hanyar da ta dace ba wajen shawo kan matsalar tattalin arziki da ’yan kasa suke fuskanta. Samar da mafita ta wucin-gadi ko bayar da tallafi ta hanyar ciyarwa ko raba babura ba ita ce tartibiyar hanyar shawo kan matsalar ba. Ana yakar talauci da rashin aikin yi ne ta hanyar ba wa ’yan kasa horo, ba tallafin kaya ba.

Babu wata kasa da ta ci gaba ta hanyar raba kayan tallafi. Shugabanni suna cutar ’yan Nijeriya ne ta hanyar fifita bayar da kayan tallafi, da nufin yin awon gaba da kudin al’umma, wadanda sun isa su samar da mafita ta dindindin ga matsalolin zamantakewa da tattalin arzikin Nijeriya.

Bisa ga irin dimbin arzikin da kasar nan take da shi, da ya hada da yawan mutane, wadda wata dama ce ta rage talauci da rashin aikin yi, inda ’yan Nijeriya, musamman matasa suke bukatar horo fiye da raba kayan tallafi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya ta ware Naira biliyan samar da mafita ta bayar da tallafi watan Ramadana kayan tallafi

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho

Hukumar Fensho ta Jihar Jigawa da Kananan Hukumomin jihar ta shirya fara aikin tantance ‘yan fansho da ke cikin tsarin.

Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, Alhaji Muhammad K. Dagaceri ne ya bayyana haka yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Gidan Fansho, inda shugabannin kungiyar ‘Yan Fansho ta Najeriya reshen Jigawa suka halarta.

A cewarsa, an shirya fara aikin tantancewar ne daga ranar Litinin, 5 ga Mayu, 2025.

Alhaji Dagaceri ya bayyana cewa, an shirya hakan ne da nufin sabunta tsarin biyan fansho tare da tabbatar da ingancin bayanai.

Ya ce, aikin tantancewar zai gyara wasu ‘yan kura-kurai da suka kunno kai a cikin shekaru uku da suka gabata, da kuma tabbatar da ingantattun bayanai a jadawalin biyan fansho.

Ya kara da cewa, wannan yunkuri ya yi daidai da kudirin jihar gwamnati na tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkokin mulki, tare da bai wa ‘yan fansho dama su gyara duk wani bayanin da bai cika ba a takardunsu.

Shi ma da ya ke jawabi, Akanta Janar na Jihar, Alhaji Abdullahi S.G. Shehu, ya jaddada cewa aikin tantancewar zai bai wa ‘yan fansho damar sabunta bayanansu da suka bace ko suka canza a takardunsu.

Saboda haka, ya bukaci dukkan ‘yan fansho daga ma’aikatun gwamnati, sassan hukumomi, kananan hukumomi da kuma hukumomin ilimi na kananan hukumomi da su halarci tantancewar a ranar da aka tsara kamar yadda yake cikin jadawalin aikin.

A jawabinsa, Shugaban kungiyar kananan hukumomi ALGON ta Jihar Jigawa, Farfesa Salim Abdurrahman, ya tabbatar da cikakken goyon baya daga shugabannin kananan hukumomi 27 domin cimma burin aikin.

Shugaban na ALGON wanda shugaban karamar hukumar Malam Madori,  Alhaji Salisu Sani ya wakilta,  ya bukaci ‘yan fanshon da su ba da cikakken haɗin kai don samun nasarar shirin.

Shi ma Shugaban hukumar, Dr. Bilyaminu Shitu Aminu, ya bukaci ‘yan fansho daga sassa daban-daban da su ba da hadin kai domin cimma burin da aka sanya, tare da jaddada cewa su ziyarci sakatariyar kananan hukumominsu domin a tantance su.

Shugaban Kungiyar ‘Yan Fansho ta Najeriya reshen Jihar Jigawa, Alhaji Umar Sani Babura, ya yi alkawarin cewa kungiyar za ta bada cikakken goyon baya domin nasarar wannan shiri.

Dukkan ‘yan fansho daga Ma’aikatun Gwamnati, Kananan Hukumomi, da Hukumomin Ilimi na Kananan Hukumomi da ke cikin tsarin  fanshon, ya zama wajibi su halarci wannan tantancewa a ranakun da aka tsara a jadawalin aikin.

 

Usman Muhammad Zaria

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya
  • Sin Na Maraba Da Karin Abokai Daga Kasa Da Kasa Su Ziyarci Kasar
  • Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji kuskure ne — Janar Chibuisi
  • NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”
  • Kasar Sin Za Ta Samar Da Dokar Da Ta Shafi Raya Kasa