Aminiya:
2025-06-14@23:29:19 GMT

A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi

Published: 13th, April 2025 GMT

Sakamakon gazawar shugabanci, bayar da tallafi na neman zama wani bangare a tarihin dimokoradiyyar Nijeriya, inda gwamnatocin jihohi da ’yan majalisu da sauran ’yan siyasa suke amfani da shi wajen cusa wa ’yan kasa ra’ayinsu na siyasa.

A duk lokacin da al’umma suka koka a kan wani mummunann yanayi da ya hada da matsin tattalin arziki da gobarar tankar mota da ambaliyar ruwa da gobara, abin da yake biyo baya shi ne gwamnati ta raba tallafin shinkafa da sauaran kayan abinci, tamkar shinkafa ita ce maganin duk wata matsala.

A wasu lokutan, a kan raba babura masu kafa uku da dabbobi a matsayin tallafi.

Makudan kudaden da gwamnatoci suke kashewa da sunan bayar da tallafi, inda ba a ganin tasirin hakan a rayuwar ’yan kasa, lamari ne da ke ci gaba da damun ’yan Nijeriya. Alal misali, makudan kudaden da gwamnatocin jihohi arewa suka ware da sunan ciyarwar watan Ramadana ya saha suka daga ’yan kasar da dama, cikinsu har da masu amfana da ciyarwar.

A yayin da Gwamnatin Jigawa ta sanar da kashe Naira biliyan 4.8, ita kuwa Gwamnatin Kano ta ware Naira biliyan 8 domin ciyarwar Ramadanan 2025. Gwamnatin Sakkwato ta ware Naira biliyan 6.7, yayin da Gwamnatin Kebbi ta ware Naira biliyan 1.5, inda Gwamnatin Neja ta ware Naira miliyan 976. A nata bangaren, Gwamnatin Yobe ta ware Naira miliyan 298. Uwa-uba, Gwamnatin Katsina ta ware Naira biliyan 10 duk don ciyarwar watan Ramadana.

Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa

Damuwar da masu ruwa da tsaki suka bayyana ita ce yadda gwamnatocin suka kashe wadannan makudan kudade da sunan shirin ciyarwar Ramadana. Misali, shirin ciyarwar Gwamnatin Jigawa an yi hadin gwiwa ne tsakanin gwamnatin jihar da kananan hukumomi bisa kaso 55 da 45. Rashin tabbacin da ke tattare da wannan shiri shi ne su wane ne ainihin wadanda suka amfana da wannan shiri na ciyarwa, sannan kuma wanne tsari aka bi wajen rabo?

A wata ziyar ba-zata da Gwaman Jihar Jigawa ya kai daya daga wuraren ciyarwar a karamar Hukumar Dutse a Ramadanan da ya gabata, ya nuna rashin gamsuwarsa dangane da tsarin da ya gani, wanda hakan ya tabbatar da sukar da al’umma suke yi a kan rashin tsarin shirin ciyarwar. Gwamna Namadi ya nuna rashin amincewarsa game da rashin tsari da karancin abincin a cibiyoyi 609 da aka tsara za su bayar da abinci kala uku ga masu rauni da talakawa 182,700 a kullum. Ya koka da cewa, ‘‘Ban gamsu ba, kodayake ban yi mamaki ba da rashin tsari da sakacin da na gani ba a yau. Ba zai yiwu ba wasu ’yan tsiraru su hana mutanenmu amfana da abin da suka cancanci su samu ba.’’

Duba da irin yadda aka tafiyar da shirin ciyarwar Ramadana, shirin cike yake da almubazaranci da kudin al’umma. Rashin tartibiyar hanyar tabbatar da wadanda suka amfana da shirin, ita ce ta ba wa cin-hancin kofar shigowa. Wannan wata sabuwar hanyar satar kudin al’umma ce cikin sauki da sunan bayar da tallafi, da ya kunshi ciyar da masu rauni a watan Ramadana.

A yayin da ba za a sa kafa a shure irin rawar da bayar da tallafin gwamnati yake takawa ba a yanayi na gaggawa, masu rauni da talakawa za su fi amfana, idan aka saka wadannan makudan kudade a harkar noma da samar da aikin yi ga matasa da mata da samar da kanan masana’antu, wadanda za su samar da mafita ta dindindin. Gwamnati ta yi wa bayar da tallafi mummunar fahimta, duba da yadda ta ba shi muhimmanci, wanda hakan ke nuna dalilin da ya sa aka kasa warware matsalolin kasa yadda ya kamata.

Ya kamata bayar da tallafi ya zamto saboda wasu dalilai na musamman, da nufin bayar da agaji na wucin-gadi, ba samar da mafita ta dindindin ba ga muhimman matsalolin kasa kamar talauci da rashin aikin yi ba. Ana bayar da tallafi ne ga mutanen da suke cikin yaki kamar a yankin Sudan da Gaza.

Shugabanni, musamman gwamnonin jihohi sun fi fifita raba tallafi a al’amuansu na gwamnati, ta yadda kusan ya zama wata hanya ta kimanta ayyukan zababbun masu rike da mukaman gwamnati, duk dai saboda sun gaza fahimtar yadda ake kimanta matsayin tattalin arzikin mutane, wanda ya hada da talauci da tallafi.

Ware makudan kudade domin ciyarwar watan Ramadana ba ita ce hanyar da ta dace ba wajen shawo kan matsalar tattalin arziki da ’yan kasa suke fuskanta. Samar da mafita ta wucin-gadi ko bayar da tallafi ta hanyar ciyarwa ko raba babura ba ita ce tartibiyar hanyar shawo kan matsalar ba. Ana yakar talauci da rashin aikin yi ne ta hanyar ba wa ’yan kasa horo, ba tallafin kaya ba.

Babu wata kasa da ta ci gaba ta hanyar raba kayan tallafi. Shugabanni suna cutar ’yan Nijeriya ne ta hanyar fifita bayar da kayan tallafi, da nufin yin awon gaba da kudin al’umma, wadanda sun isa su samar da mafita ta dindindin ga matsalolin zamantakewa da tattalin arzikin Nijeriya.

Bisa ga irin dimbin arzikin da kasar nan take da shi, da ya hada da yawan mutane, wadda wata dama ce ta rage talauci da rashin aikin yi, inda ’yan Nijeriya, musamman matasa suke bukatar horo fiye da raba kayan tallafi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya ta ware Naira biliyan samar da mafita ta bayar da tallafi watan Ramadana kayan tallafi

এছাড়াও পড়ুন:

Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi

Tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi, ya ce har yanzu Najeriya ba ta kai matsayin cin ribar cikakkiyar dimokuraɗiyya ba, duk da cewa an dawo mulkin farar hula shekaru 26 da suka gabata.

Yayin wata tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels, domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya, Fayemi ya bayyana cewa duk da cewa ana gudanar da zaɓe a kai a kai a ƙasar, har yanzu an rasa muhimman abubuwan da suka kamata su kasance a tsarin dimokuraɗiyya na gaskiya.

Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna

“Bai kamata mu rikita gudanar da zaɓe da aiwatar da dimokuraɗiyya ba,” in ji shi.

“Abin da muka samu a 1999 shi ne ’yancin zaɓar shugabanni, amma hakan kawai ɓangare ne guda ɗaya.

“Abin da muke da shi mulkin farar hula ne, ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba.”

Ya ce an samu ci gaba a ƙarƙashin gwamnatoci daban-daban tun daga baya, amma har yanzu Najeriya na buƙatar ƙarfafa al’adar dimokuraɗiyya da sauye-sauyen da suka dace.

Fayemi ya kuma tuna da lokacin da ya kasance ɗaya daga cikin masu fafutukar dimokuraɗiyya a zamanin mulkin soja, musamman a lokacin marigayi Janar Sani Abacha.

Ya bayyana yadda suka gudanar da shirye-shirye a wani gidan rediyo a aka ɓoye, don ƙalubalantar gwamnatin soji.

“Ba wai rashin tsoro ba ne, mun san hatsarin da ke tattare da lamarin, amma mun yi imani da abin da muke yi,” in ji shi.

“Na taɓa ɗaukar na’urar watsa shirye-shiryen rediyon Kudirat a cikin jirgin Air France da ya sauka a Legas lokacin da fafutukar ta yi zafi. Wannan kaɗai na iya jefa ni cikin hatsari.”

Ya ce waɗanda suka mutu a lokacin ba don sakaci suka rasa rayukansu ba, sai don sun gaskata ƙudurinsu na ganin an samu ’yanci.

Fayemi ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu bisa karrama wasu daga cikin waɗanda suka fafata wajen dawo da dimokuraɗiyya.

Sai dai ya nuna damuwa cewa wasu da dama da suka taka muhimmiyar rawa a bayan fage ba a karrama su ba.

“Mutane da dama sun sa rayuwarsu cikin hatsari. Su ma sun cancanci a yaba musu.

“Ba daidai ba ne a girmama waɗanda ake gani a manta da waɗanda suka bayar da gudunmawarsu a bayan fage.”

Maganganun Fayemi sun haifar da zazzafar muhawara kan yadda Najeriya ke da buƙatar ci gaba kafin a kira ta da ƙasar da ke da cikakkiyar dimokuraɗiyya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki