Nigeria: Wani Bom Da Ya Tashi A Maiduguri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 7
Published: 13th, April 2025 GMT
Rahotanni da suke fitowa daga Nigeria sun ce, a kalla mutane 7 su ka rasa rayukansu, yayin da wasu da dama su ka jikkata sanadiyyar fashewar wasu abubuwa masu karfi akan hanyar Damboa-Zuwa Maiduguri.
Rahotannin sun ce abubuwan su fashe ne dai a lokacin da wasu ayarin motoci da suke wucewa ta hanyar tare da rakiyar sojoji a jiya Asabar da hakan ya haddasa asarar rayuka da kuma jikka.
Hanyar Damboa zuwa Maiduguri tana zuwa kananan hukumomi da dama a kudancin Jahar ta Borno, a lokaci daya kuma yanki ne da ya yi kaurin suna a matsayin matsugunin ‘yan Bokoharam.
An dade da rufe hanyar saboda matsalar tsaro, amma gwamnatin Babagana zulum ta sake bude ta, da kuma dawo da zirga-zirgar ababen hawa zuwa Damboa,Chibok da kuma wasu kananan hukumomi da suke a kudancin Jahar.
Ana barin matafiya su bi ta hanyar ne sai biyu a mako daya, bayan sojoji sun yi sintiri da kuma tabbatar da cewa ba a dasa abubuwan fashewa ba. Kusan shekaru biyu kenan ana yin haka. Tuni dai aka dauki wadanda su ka jikkata da ba a tantance adadinsu ba zuwa asibitin cikin Maiduguri domin yi musu magani.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ben Gafir Ya Bukaci Gwamnatin HKI Ta Mamaye Yankin Gaza Gaba daya
Ministan tsaron cikin gida na HKI Itamar Ben-Gvir ya yi kira ga babban murya kan cewa dole ne HKI ta mamaye dukka zirin gaza ta kuma kori falasdinawa da suke cikinsa.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalato Ben Gafir yana fadar haka a jiya ya kuma kara da cewa mamaye gaza da kuma yankin yamma da kogin Jordan da kuma shi ne kawai zai sa a samar da kasar yahudawan zalla inda babu ba falasdine ko guda a yankunan guda biyu.
Kiran nasa dai ya gamu da maida martani daga yan siyasa a ciki da wajen HKI.
Tun shekara ta 2023 ne gwamnatin HKI take son mamyar zirin gaza ta kuma kori Falasdiwa a yankin. Bayan yaklin da kungiyar Hamas ta fara a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023
Amma da alamun yahudawan sun kasa, saboda har yanzunn kungiyar Hamas tan gaza kuma tana ci gaba da halaka sojojin yahudawan a cikinsa.
A halin yanzu dai yahudawan sun kashe falasdinawa fiye da dubu 50, kuma suna ci gaba da kashesu a duk ranar All.. musamman a wajen tarkon karban abinci da suka kafa masu.