Ya soki masu ra’ayin cewa dimukradiyya wani sharadi ne na ci gaba, yana mai cewa “karya ne” shi akwai wata kasa da ta ci gaba a karkashin tsarin dimukradiyya?.

Burkina24 ta nakalto cewa “Babu wata kasa da za a iya bayyanawa da ta ci gaba a dimukradiyya.

Ya ci gaba da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da sadarwa, bayyanawa, da kuma fahimtar da mutane mene ne juyin juya hali.

Traore ya yi fice wajen yanke shawarar ce bayan hayewarsa a matsayin shugaban kasar da ke yammacin Afirka.

Shugaban mai shekaru 37 da haihuwa wanda ya hau karagar mulki a watan Satumban 2022 ta hanyar juyin mulkin da ya hambarar da shugaban kasar na wucin gadi Paul-Henri Damiba kwanan nan ya yi watsi da tayin Saudiyya na gina masallatai 200 a kasarsa.

Ya bukaci kasar Musulunci da ta gwammace ta saka hannun jari a wasu muhimman ayyukan more rayuwa wadanda za su amfani al’ummarsa kai tsaye.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

Yaƙin M23 Ya ci Gaba a Congo Duk da Sulhu da Rwanda

Bayan da ƙasashen biyu maƙwabtan juna na Congo da Rwanda suka sanya hannu a yarjejeniyar zaman lafiya da Donald Trump ya bayyana a matsayin mai cike da tarihi, jagoron na Amurka ya jinjinawa shugabannin ƙasashen biyu waɗanda ya ce sun yi hangen nesa wajen amincewa da kawo ƙarshen zubar da jinin dubban mutane tsawon shekaru.

An dai haska wannan zaman sanya hannu kai tsaye ta gidajen talabijin, inda shugabannin biyu wato Felix Tshisekedi na Jamhuriyyar Congo da Paul Kagame na Rwanda suka rattaɓa hannu a yarjejeniyar a gaban idon Donald Trump can a birnin Washington.

A cewar Trump shugabannin biyu sun ajje banbance-bambancen da ke tsakaninsu wajen rungumar zaman lafiya don jama’arsu.

Sai dai an sanya hannu a yarjejeniyar can a Washington dai dai lokacin da ake ganin ci gaban yaƙi tsakanin Sojin Congo da mayaƙan M23 da Rwanda ke marawa baya a kudancin lardin Kivu.

Babu dai wakilcin M23 a wannan tattaunawa ta Washington, hasalima basu aminta da yarjejeniyar da ka cimma a zaman ba, maimakon haka suna halartar nasu taron na daban wanda Qatar ke jagorantar sulhunta su da Congo a birnin Doha.

Masu sharhi na ganin  abu ne mai matuƙar wahala, yarjejeniyar ta birnin Washington ta yi tasiri wajen kawo ƙarshen wannan yaƙi na shekaru.

Yarjejeniyar na zuwa a dai dai lokacin da Amurka ke son zuba jari a ɓangaren haƙar ma’adinai a Congo inda a gefe guda itama Qatar ke faɗaɗa shirinta na zuba jari a ƙasashen Afrika.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan
  • Yaƙin M23 Ya ci Gaba a Congo Duk da Sulhu da Rwanda
  • Putin Na Rasha Ya Ce; Kasarsa Da India Za Su Kara Girman Kasuwancinsu
  • Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa
  • ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • Gwamnatin Gombe da UNICEF sun tallafa wa yara masu fama ƙarancin abinci mai gina jiki
  • Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump?
  • Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya
  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya