Shugaban Jami’ar TTarayyada ke Dutse a Jihar Jigawa, Farfesa Abdulkarim Sabo Muhammed ya amince da nadin Malam Abdullahi Yahaya Bello, a matsayin Daraktan riko na Jami’ar daga ranar 1 ga watan Maris na 2025.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da magatakardar jami’ar, Alhaji Abubakar Mijinyawa ya rabawa manema labarai a Dutse.

Sanarwar ta taya Malam Abdullahi murna tare da yi masa addu’ar Allah ya ba shi nasara wajen sauke nauyin da aka dora masa.

Malam Abdullahi Yahaya Bello shi ne ya kafa sashen yada labarai da hulda da jama’a na jami’ar a shekarar 2012 a matsayin jami’in hulda da jama’a na Jami’ar na farko.

Sanarwar ta ci gaba da bayyana cewa, ya ci gaba da zama mataimakin daraktan yada labarai da hulda da jama’a na a shekarar 2023 kafin nadin da yake yi a yanzu a matsayin Mukaddashin Daraktan kula da hulda da jama’a na Jami’ar Tarayya ta Dutse.

“Ya halarci tarurrukan horaswa da bita kan kafafen yada labarai da hulda da jama’a da dama, kuma memba ne a Cibiyar Hulda da Jama’a ta Najeriya (NIPR), Memba a Kungiyar ‘Yan Jarida ta kasa (NUJ), hakazalika Memba, da sauran kungiyoyin ilimi da dama.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa

Haka kuma, ya taɓa zama mataimakin kocin Super Eagles lokacin da Jose Peseiro ke jan ragamar ‘yan wasan Nijeriya.

A kakar bara ta NPFL, ya jagoranci Kano Pillars ta ƙare a matsayi na 9.

Ko da yake Usman bai bayyana cikakken dalilin saukarsa ba, masu sharhi a wasan ƙwallon ƙafa na ganin matsin lamba daga magoya baya da rashin nasara sun taka rawa.

Har yanzu, ƙungiyar ba ta fitar da sabuwar sanarwa kan wanda zai maye gurbinsa ba.

Masu sha’awar wasan ƙwallon ƙafa a Kano na fatan za a kawo sabon kocin da zai dawo da martabar Pillars a wasannin gaba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa