Gwamnatin Tarayya ta ce ta gano irin muhimmiyar gudunmuwar da kungiyoyin hadaka ke takawa wajen bunkasa tattalin arziki da ci gaban al’umma, da kuma karfafa jama’a a kasar.

 

Karamin Ministan Noma da Tsaron Abinci, Dakta Aliyu Sabi Abdullahi, ya bayyana hakan yayin kaddamar da shirin horo na musamman ga shugabanni, kwamitocin gudanarwa, da manajoji na kungiyoyin hadaka a Najeriya, wanda aka shirya a Kaduna.

 

A cewar Kungiyar Hadaka ta Duniya (International Cooperative Alliance), sama da kashi 12% na al’ummar duniya suna cikin daya daga cikin kungiyoyin hadaka miliyan 3 a duniya.

 

Kungiyoyin hadaka suna nada muhimmiyar gudunmuwa wajen bunkasa tattalin arziki mai dorewa, inda suke samar da ayyukan yi da damammaki ga mutane miliyan 280, wanda ya kai kimanin kashi 10% na ma’aikatan duniya.

 

Kungiyoyin hadaka 300 mafi girma da kamfanonin taimakon juna suna samar da kudaden shiga har dala tiriliyan 2.4, kamar yadda rahoton World Cooperative Monitor na 2023 ya nuna.

 

A cewar Karamin Ministan Noma da Tsaron Abinci, Dakta Aliyu Sabi Abdullahi, domin cika burin farfado da wannan bangare, Gwamnatin Tarayya ta kuduri aniyar samar da horo da damammakin ci gaban shugabanni da manajoji na kungiyoyin hadaka a jihohi 36 na Tarayya ciki har da Babban Birnin Tarayya (FCT).

 

Ya ce yayin da gwamnati ke aiwatar da Shirin Sabon Fata don bangaren kungiyoyin hadaka, tana daukar matakan gyara da farfado da tsarin domin mayar da martabar kungiyoyin hadaka a matsayin mai karfi wajen ci gaban zamantakewa da tattalin arziki a Najeriya.

 

Dakta Aliyu Sabi Abdullahi ya kuma bayyana cewa gyaran zai mayar da hankali kan dubawa da gyaran dokar Nigeria Cooperative Act don daidaita ta da kyawawan dabi’un duniya da yanayin gida.

 

Samar da tsari mai kyau na lura da gudanarwar kungiyoyin hadaka don tabbatar da gaskiya da rikon amana.

 

Samar da tsare-tsaren sa ido don kawar da kungiyoyin hadaka na bogi da masu zamba.

Ya kuma yaba wa Shugaban Kwalejin Hadaka ta Tarayya Kaduna, Dakta Ibrahim Auwal, bisa kaddamar da wannan shirin horo na musamman da ya yi daidai da tsarin gyara da farfado da bangaren.

 

A nasa jawabin, Shugaban Kwalejin, Dakta Ibrahim Auwal, ya ce horon zai baiwa mahalarta damar samun kwarewa da ilimin da ake bukata don ci gaban kungiyoyinsu da karfafa al’ummomin da suke wakilta.

 

Ya jaddada cewa kungiyoyin hadaka su ne ginshikan karfafa tattalin arziki da hade-haden zamantakewa, da ci gaba mai dorewa.

 

Cov: Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamnati Gwamnati Ta Tabbatar da Kungiyoyin Hadaka a Matsayin Ginshikin Ci gaban Al umma Matsayin Tabbatarda

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta bayyana cewa: Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila’ tana aiwatar da kisan kiyashi kan Falasdinawa ana gani kai tsaye a tauraron dan Adam

Kungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty International a yau Talata ta yi Allah wadai da shirun da duniya ta yi game da yadda gwamnatin yahudawan sahayoniyya ‘yan mamaya take aiwatar da kisan kiyashi a zirin Gaza, kai tsaye duniya na gani ta hanyar tauraron dan Adama.

A yayin gabatar da rahoton shekara-shekara na kungiyar ta Amnesty kan kare hakkin bil’adama a duniya Agnes Callamard, sakatariyar kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International, ta ce tun ranar 7 ga watan Oktoban shekara ta 2023, duniya ke kallon yadda ake aiwatar da kisan kare dangi kai tsaye a tauraron dan Adam a Zirin Gaza.

Ta kara da cewa, “Sun ga kasashe kamar babu abin da zasu iya saboda da rauni” tare da nuna cewa “gwamnatin mamayar Isra’ila na kashe dubban Falasdinawa maza da mata, ta hanyar kisan kiyashi kan dukkanin iyalai da suka hada da kananan yara, da lalata gidaje, rusa cibiyoyin tsare rayuka, rusa asibitoci da cibiyoyin ilimi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Ta ƙaddamar Da Sabon Shafin Intanet Don Inganta Sayayya A Tsakanin Ma’aikatunta 
  • Yanayin Rudani Na Tsawon Kwanaki 100 Kashedi Ne Ga Amurka
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ
  • Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
  • Shin Amurka Na Iya Komawa Kan Kadaminta A Matsayin Cibiyar Masana’antun Duniya?
  • Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Daidaita Samar Da Guraben Ayyukan Yi Da Raya Tattalin Arziki
  • Al-Shara Ya Ki Abincikewa Da Tsarin Tarayya Wanda Kurdawan Kasar Siriya  Suke Bukata
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano