An gudanar da taron dandalin ciniki tsakanin Sin da Habasha kana taron sa kaimi ga dandalin baje kolin tsarin samar da kayayyaki na kasa da kasa wato CISCE karo na 3 a jiya Litinin a Addis Ababa, hedkwatar kasar Habasha.

Kwamitin sa kaimi ga cinikin Sin da ketare da kwamiti mai kula da harkar zuba jari na Habasha da kungiyar kasuwanci da kungiyar sana’o’in Habasha sun gudanar da taro mai taken “Shiga Habasha: Habaka hadin gwiwar tsarin samar da kayayyaki tsakanin Sin da Afirka” cikin hadin kai.

Inda wakilai fiye da 200 daga bangarorin gwamnatoci da ciniki da tattalin arziki da kafofin yada labarai da sauransu suka halarci taron.

Jakadan Sin dake Habasha Chen Hai ya gabatar da wani jawabi, inda ya ce, dandalin CISCE irinsa na farko a duniya dake mai da hankali kan tsarin samar da kayayyaki a duniya, zai samar da wani muhimmin dandali ga mabambantan kamfanonin kasashen duniya wajen habaka kasuwaninsu a ketare da jawo jari daga waje da mu’amalar kimiyya da daga kimar kasashensu da dai sauransu.

Darektan kwamiti mai kula da zuba jari na Habasha Zeleke Temesgen ya ce, a halin yanzu, Sin ta zama daya daga cikin abokai mafi karfi a bangaren ciniki da zuba jari ga Habasha. Yana fatan ’yan kasuwan kasar Sin za su nazarci babbar damar zuba jari a kasarsa, da kafa huldar abokantaka mai karfi da dorewa tsakaninsu, a cewarsa. Yana mai fatan shigowar Sin wannan bangare zai gaggauta bunkasa tattalin arzikin kasar, har ma da samar da karin guraben aikin yi da ingiza samun wadata cikin hadin gwiwa baki daya. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Yaba Da Kwazon Shugaba Bola Ahmad Tinubu

Masu ruwa da tsakin Arewa sun yaba da kwazon Tinubu, inda suka bukaci a kara karfafa gwiwar ‘yan kasa a taron Kaduna.

 

Masu ruwa da tsaki a Arewacin Najeriya sun yaba wa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa irin ci gaban da ta samu wajen cika alkawuran zabe, musamman a muhimman batutuwan da suka shafi tsaron kasa, samar da ababen more rayuwa, da sake fasalin tattalin arziki.

 

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban darakta na gidauniyar tunawa da Sardaunan Sakkwato Sir Ahmadu Bello, Engr. Abubakar Gambo Umar, kuma ya rabawa manema labarai a karshen taron tattaunawa na kwanaki biyu da aka gudanar a Arewa House, Kaduna.

 

Ya yaba wa gwamnatin Shugaba Tinubu saboda nuna gaskiya da kuma kyakkyawan aiki, yayin da ta bukaci ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da daidaito, adalci, da hadin gwiwar yanki.

 

Mahalarta taron sun kuma yaba da irin ci gaban da gwamnatin ta samu kan manyan ayyuka irin su bututun iskar gas na AKK, da aikin hako mai na Kolmani, da kuma ayyukan noman rani na karkara wadanda ke amfana da al’ummar Arewa kai tsaye.

 

Ya tabbatar da cewa, kawancen ’yan kasa da na gwamnati na da matukar muhimmanci wajen dorewar dimokuradiyya, da hadin kan kasa, da kuma ci gaba mai dorewa.

 

Har ila yau, ya haifar da damuwa game da matsalolin da ke addabar yara da ba sa zuwa makaranta a Arewa da kuma gaggawar karfafa sarkar darajar noma don samar da ayyukan yi da samar da abinci.

 

Daga cikin muhimman kudurori, taron ya yi kira da a samar da tsare-tsare na yau da kullum na gwamnati da ‘yan kasa, a matakin kasa da na jihohi.

 

Har ila yau, ta ba da shawarar inganta harkokin zuba jari a fannin ilimi, musamman don magance tsarin Almajirai da kuma matsalar rashin makaranta da ke addabar Arewacin Nijeriya.

 

Mahalarta taron sun bayar da shawarar kara hadin gwiwa tsakanin gwamnatocin tarayya da na jihohi, da goyon bayan kishin kasa, dabarun da suka shafi al’umma don sauye-sauyen tattalin arziki da tsaro, tare da karfafa gwiwar kungiyoyin farar hula, na gargajiya, da shugabannin addinai da su kara taka rawa wajen bayar da shawarwarin manufofin jama’a.

 

Shugaban kungiyar gwamnonin Najeriya kuma gwamnan jihar Kwara Abdulrahman Abdulrazaq ne ya wakilci shugaba Bola Tinubu a wajen taron.

 

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya wakilci Dakta Aliyu Modibbo Umar, mai ba da shawara na musamman kan ayyuka na musamman, yayin da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya kasance babban mai masaukin baki.

 

Gwamnan jihar Gombe kuma shugaban kungiyar gwamnonin jihohin Arewa, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya halarta a matsayin babban bako na musamman.

 

Manyan jami’an gwamnatin tarayya sun hada da Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Sanata George Akume, wanda ya jagoranci tawagar. Sauran manyan wadanda suka halarci taron sun hada da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, mambobin majalisar ministocin tarayya, shugabannin hukumomin tsaro, da manyan jami’an tsaro daga Arewacin Najeriya.

 

A jawabin da ya gabatar, Farfesa Tijjani Mohammed Bande, ya bayyana yadda Najeriya ke da karfin gwiwa a cikin kalubale kamar rashin tsaro, talauci, da gibin ilimi.

 

Ya bukaci shugabannin Arewa da su tabbatar da muradun su a cikin tsarin kasa ta hanyar daidaitawa da ingantattun manufofin ci gaba masu amfani ga gamayya.

 

Babban zaman taron ya tattauna batutuwan da suka shafi kasa baki daya da suka hada da tsaro, shugabanci, farfado da tattalin arziki, noma, samar da ababen more rayuwa, da ci gaban bil Adama.

 

Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • INEC Ta Gudanar da Taron Masu Ruwa da Tsaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi na Babura/Garki
  • Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres
  • An Yaba Da Kwazon Shugaba Bola Ahmad Tinubu
  • Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana
  • Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi
  • Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba za mu amince da kafa ƙasar Falasɗinu — Birtaniya
  • An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025