An gudanar da taron dandalin ciniki tsakanin Sin da Habasha kana taron sa kaimi ga dandalin baje kolin tsarin samar da kayayyaki na kasa da kasa wato CISCE karo na 3 a jiya Litinin a Addis Ababa, hedkwatar kasar Habasha.

Kwamitin sa kaimi ga cinikin Sin da ketare da kwamiti mai kula da harkar zuba jari na Habasha da kungiyar kasuwanci da kungiyar sana’o’in Habasha sun gudanar da taro mai taken “Shiga Habasha: Habaka hadin gwiwar tsarin samar da kayayyaki tsakanin Sin da Afirka” cikin hadin kai.

Inda wakilai fiye da 200 daga bangarorin gwamnatoci da ciniki da tattalin arziki da kafofin yada labarai da sauransu suka halarci taron.

Jakadan Sin dake Habasha Chen Hai ya gabatar da wani jawabi, inda ya ce, dandalin CISCE irinsa na farko a duniya dake mai da hankali kan tsarin samar da kayayyaki a duniya, zai samar da wani muhimmin dandali ga mabambantan kamfanonin kasashen duniya wajen habaka kasuwaninsu a ketare da jawo jari daga waje da mu’amalar kimiyya da daga kimar kasashensu da dai sauransu.

Darektan kwamiti mai kula da zuba jari na Habasha Zeleke Temesgen ya ce, a halin yanzu, Sin ta zama daya daga cikin abokai mafi karfi a bangaren ciniki da zuba jari ga Habasha. Yana fatan ’yan kasuwan kasar Sin za su nazarci babbar damar zuba jari a kasarsa, da kafa huldar abokantaka mai karfi da dorewa tsakaninsu, a cewarsa. Yana mai fatan shigowar Sin wannan bangare zai gaggauta bunkasa tattalin arzikin kasar, har ma da samar da karin guraben aikin yi da ingiza samun wadata cikin hadin gwiwa baki daya. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Fara Baje Kolin Kayakin Da Ake Kerawa A Iran Tare Da Taron Iran Da Afirka Karo Na Uku

An fara kasuwar baje koli na kayakin kasuwancin da ake samarwa a cikin Iran ko IRAN EXPO 2025, karo na 3 a nan Tehran.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa kasuwar baje koli na Iran EXPO 2025 zai jawa masu zuna jari daga kasashen Afirka.

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya fadawa kamfanin dillancin labaran IP kan cewa Kasuwar ta bana dai, za ta tara kamfanonin  masu samar da kayaki daga yankuna daban daban na kasar Iran da dama, kuma akwai fatan cewa wannan kasuwar ta zama mabudi ga kyautatuwan tattalin arzikin kasar.

EXPO dai ita ce kasuwar baje koli na kayakin kasar Iran mafi girma wanda ake gudanarwa a ko wace shekara, sannan daga nan take samun kasuwa a kasashen duniya. Kuma yan kasuwa daga kasahe fiya da 100 ne  suka shigo kasar don halattan kasuwar.

 Esma’il Bakaee, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya ce ya na fatan a wannan  kasuwar, kasashen Afirka da Iran za su amfani juna a harkokin kasuwancin da ake bunkasa a tsakaninsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya za ta karɓi baƙuncin Gasar Karatun Alkur’ani ta Duniya a karon farko 
  • Gwamnati Ta ƙaddamar Da Sabon Shafin Intanet Don Inganta Sayayya A Tsakanin Ma’aikatunta 
  • Kar A Mika Wuya Ga “Damisar Takarda”
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • An Fara Baje Kolin Kayakin Da Ake Kerawa A Iran Tare Da Taron Iran Da Afirka Karo Na Uku
  • Shin Amurka Na Iya Komawa Kan Kadaminta A Matsayin Cibiyar Masana’antun Duniya?
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Daidaita Samar Da Guraben Ayyukan Yi Da Raya Tattalin Arziki
  • Al-Shara Ya Ki Abincikewa Da Tsarin Tarayya Wanda Kurdawan Kasar Siriya  Suke Bukata