Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu
Published: 25th, October 2025 GMT
Sauyin shugabannin tsaro dai ya nuna matakin da Tinubu ke ɗauka wajen sake fasalin tsaro, amma kuma ya buɗe sabon babi na tattaunawa kan yadda ake kula da tsofaffin hafsoshin da suka ba ƙasa hidima tsawon shekaru.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci
Gwamna Raɗɗa ya ƙara da cewa wannan zaman sulhu da ɓarayin daji da ake yi al’umma ce take yi ba wai gwamnati ba, ita gwamnati tana iya yin sulhu da ɗan bindigar da ya tuba ya yarda da zaman lafiya kuma ya ajiye mukaminsa.
A cewarsa, rawar da gwamnati take iya takawa shi ne, ta ƙarfafa zaman lafiya, sannan ta tabbatar an bi doka da oda a cikin al’umma. Ya ce abubuwa da gwamnati ke lura da su shi ne, al’umma ta mori zaman lafiya domin bunƙasar tattalin arziki da sauran su.
Tunda farko a jawabinsa, kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida, Hon. Nasiru Mu’azu Danmusa ya bayyana cewa Gwamna Raɗɗa ya rage ƙarfin harkokin rashin tsaro a Jihar Katsina.
Haka kuma ya bayyana cewa wannan ne karo na uku da aka ƙaddamar da bikin yaye dakarun tsaro na Malam Dikko Raɗɗa, sannan za a sake ƙaddamar da sauran a watan Nuwambar wannan shekarar idan Allah ya kai mu rai da lafiya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA