Leadership News Hausa:
2025-10-25@13:28:32 GMT

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi

Published: 25th, October 2025 GMT

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi

Ƙarfafa Ginshiƙin Tattalin Arziki

A ƙarƙashin jagorancin hangen nesa na Dakta Okpanachi, DBN ta bayar da sama da Naira tiriliyan 1.1 a matsayin lamuni ga fiye da MSMEs 700,000 a faɗin Nijeriya.

Abin da ya sa waɗannan lambobin suka zama na musamman shi ne labarin ɗan’Adam da suke bayyana: Kashi 65 cikin ɗari na masu amfana mata ne da matasa,

Kuma tallafin ya ƙirƙiri ko ya tabbatar da kimanin ayyukan yi miliyan 1.

2 a ƙasa baki ɗaya.

Waɗannan ba lambobi ne kawai ba; Labarai ne na  maɗinka a Aba, masu sarrafa shinkafa a Kebbi, masu ƙirƙirar fasaha a Legas, da masu sana’o’i a Kaduna waɗanda yanzu za su iya gudanar da kasuwanci mai ɗorewa saboda wani ya yarda da basirarsu.

Falsafar jagoranci ta Dakata Okpanachi tana da sauƙi: ingancin samun kuɗi shi ne igancin ƙasa. Ta hanyar ƙarfafa MSMEs, ginshikin gaskiya na tattalin arzikin Nijeriya, ya taimaka wajen yaɗa arziki zuwa wurare da bankunan gargajiya da a da can ba sa kula da su ba.

 

Gina Banki Don Ci Gaba, Ba Domin Dogaro Da Tallafi Ba

Dakta Okpanachi ya kawo tsari, ladabi, da manufa mai bayyana: ya sanya DBN zama misali wajen tallafin ci gaban kasuwanci a Afirka.

Ya gabatar da samfurin bayar da lamuni mai amfani da bayanai da fasaha, wanda ke ƙara gaskiya, rage haɗarin bashi, da faɗaɗa damar samun kuɗi ga sassa da ba a kulawa da su sosai. Ta hanyar haɗin gwiwa da cibiyoyin kuɗi fiye da 65, yanzu DBN na ba da tallafin kuɗi mai rahusa da tsawon lokaci ga ƙananan kasuwanci a kowace jiha.

Wannan samfurin ya sami girmamawa a duniya, inda ya sanya DBN zama mai ba da kuɗi kuma malamin banki wanda ke ƙarfafa tsarin kuɗi maimakon yin gogayya da shi.

“Ba mu zo don mamaye kasuwa ba; mun zo ne don zurfafa ta.”

 

Ƙirƙire-Ƙirƙire a Matsayin Dabarun Ci Gaba

Lokacin shugabancin Dr Okpanachi sai ya zama ya cika da ƙirƙire-ƙirƙire, ba wai a kalmar jan hankali kawai ba, har ma da tsarin aiki.

Ya jagoranci ayyukan sauyin dijital da ke ba bankuna da cibiyoyin micro-finance masu haɗin gwiwa damar sarrafa lamunin MSMEs cikin inganci, tare da sa ido kan tasirinsu a lokaci na ainihi.

Haka kuma, ya ƙaddamar da Tsarin Gudanar da Muhalli da Al’umma  na DBN, wanda ke tabbatar da cewa kowanne aikin da aka tallafa ya dace da manufofi masu ɗorewa, daga makamashi mai sabuntawa, zuwa kamfanonin da mata ke jagoranta, da aikin noma mai ɗorewa.

A fannin yabo ga waɗannan nasarori kuwa, abokan haɗin gwiwa na duniya ciki har da Bankin Duniya, da AfDB, da Bankin Zuba Jari na Turai sun faɗaɗa haɗin gwiwar su da DBN, suna yabawa da gaskiyar shugabanci da ƙwarewar gudanarwa.

 

Ɗangaren ɗan’Adam na Harkar Kuɗi

Baya ga lambobi, akwai sadaukarwar Dr Okpanachi wajen gina mutane, ba kawai jadawalin kuɗi ba.

A ƙarƙashin kulawarsa, Shirin Horar da ‘Yan Kasuwa na DBN (Entrepreneurship Training Programme – ETP) ya horar da fiye da ‘yan kasuwa 9,500 da ƙwarewar aiki a fannin haɓaka kasuwanci, shugabanci, da ilimin kuɗi.

Masu kammala shirin ETP sun ci gaba da ƙirƙirar ayyukan yi, samun tallafin kuɗi, da gina kamfanoni masu ɗorewa, suna nuna cewa haɓaka ƙwarewa yana da muhimmanci kamar samun kuɗi.

Ta wannan haɗin gwiwar kuɗi da jagoranci, DBN ta zama banki kuma aji, wurin da kasuwanci ke haɗuwa da ƙarfafawa.

 

Tafiyar Ladabi Da Hangen Nesa

Duk da cewa fiye da shekaru 30 na ƙwarewa a harkar banki wanda ya haɗa kasuwanci, sayarwa ga jama’a, da bankin ci gaba, Dr Okpanachi ya haɗa ƙwarewar fasaha da hankalin ɗan’Adam cikin ƙwarewa ta musamman.

Kafin shiga DBN, ya riƙe manyan muƙamai a Zenith Bank da Bank of Industry, inda ya ƙware wajen gina cibiyoyi da jagorancin dabaru.

Ya samu digiri daga Jami’ar Ahmadu Bello da Jami’ar Legas, har ma da PhD a Fannin Gudanar da Kasuwanci (Business Administration).

Mai kammala karatu daga Harɓard Business School da Alliance Manchester Business School, shi ma’aikaci ne na Chartered Institute of Bankers of Nigeria (CIBN) kuma mai tasiri a cikin al’ummar bankin ci gaban Afirka.

Labarinsa shi ne na mai sauƙin gyara tsarin da ya sami damar yin tasiri a ƙasa baki ɗaya ba tare da yin hayaniya ba.

 

Gado Na Ci Gaba Mai Ɗorewa

A ƙarƙashin jagorancin Dr Okpanachi, DBN ta zama ginshiƙi a tsarin tallafin kuɗi ga MSMEs na Nijeriya — cibiyar misali wacce ke haɗa riba da manufa.

Juriya da ta nuna a lokacin girgizar tattalin arziki, annobar duniya, da rashin tabbas na kuɗaɗen gwamnati ya nuna tsayuwarsa kan ingantaccen shugabanci da tsare-tsaren dogon lokaci fiye da ganin abubuwa na ɗan lokaci.

Yanzu, jadawalin kuɗi na DBN ba a auna shi ne kawai a Naira da Kobo kawai ba, an ma farfaɗo da rayuka, kasuwancin da aka farfaɗo da su, da al’ummomin da aka ƙarfafa.

“Ci gaban ƙasa ba kalma ce kawai ba, shi bambanci ne tsakanin rayuwa yin samun ɗinbin nasara.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin October 25, 2025 Manyan Labarai Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025 Gbenga Olu Komolafe October 25, 2025 Manyan Labarai Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025 October 25, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

Tawagar kamfanin na Rano Air a wurin ganawa da gwamnan, ta haɗa da Babban Manajan (Ayyuka), Abah O. Godwin; da Accountable Manager Alhaji Lawal Sabo Bakinzuwo; da Shugaban Sashin Ayyuka na ƙasa Bashir Abdullahi Wudilawa; da Shugaban Sashin Bunƙasa Harkokin Kasuwanci na kamfanin, Auwal Sulaiman Ubale.

Jami’an kamfanin sun tabbatarwa gwamnan cewa kamfanin na Rano Air zai samar da nagartacciyar hidima abar dogaro, mai inganci kuma mai haba-haba ga kwastomomi, ta yadda za a samu sauƙin tafiye-tafiyen kasuwanci da bunƙasa harkokin tattalin arziki a faɗin jihar da Arewa Maso Gabas baki ɗaya.

“Gwamna Inuwa Yahaya ya yi maraba da wannan ci gaba, inda ya bayyana hakan a matsayin wata shaida kan yadda Jihar Gombe ke da zaman lafiya da kwanciyar hankali kuma jihar da ke maraba da harkokin kasuwanci,” sanarwar ta naƙalto.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya October 24, 2025 Labarai Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi October 24, 2025 Labarai Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025, Injiniya Abdullahi Sule October 24, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu
  • Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025 Gbenga Olu Komolafe
  • Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa
  • Ƙungiya ta tallafa wa ɗaliban makarantar masu buƙata ta musamman a Gombe
  • Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe
  • Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi
  • Gwarzuwar Shekarar 2025 Sanata Oluremi Tinubu
  • Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina