Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba
Published: 25th, October 2025 GMT
Mahalifinsa, Chief Thomas Osen Ekpemupolo, da mahaifiyarsa, Mrs. Ewe Ekpemupolo, sun rayu cikin al’umma mai arziƙin mai a lokacin da ake tsaka da nema a yi wa yankinsu adalci. Daga cikin wannan rikicewar ya taso mutum wanda daga baya zai zama ɗan gwagwarmayar Niger Delta don neman daraja, adalci, da samun ikon gashin kai.
A tsakiyar shekarun 1990, arzikin mai na Nijeriya yana samu wadata a wasu wurare amma ya zama ana barin al’ummomi masu arziƙin mai cikin talauci, gurɓawa, da kuma rashin muryar magana. Ga matashin Tompolo, yin shiru wannan bai zama zaɓi ba.
Gwagwarmaya Da Juyin Juya Hali
A Ƙaramar Hukumar Kudu maso Yammacin Warri, daga Ogbe-Ijoh (garin Ijaw) zuwa Ogidigben (garin Itsekiri), an yanke shawarar da ta haifar da tashin hankali na ƙabilanci kuma ta ƙwace ikon alama daga wata ƙabilar baki ɗaya.
Tompolo ya sayar da kusan duk abin da yake da shi, gidaje uku, motar Mercedes Benz Ɓ-Boot, da jiragen ruwa da dama, don samar da kuɗi ga yakin neman gyara wannan rashin adalci. Jarumtarsa ta ja hankalin mutane, tana kuma haifar da tsoro.
A ƙarshe, a ƙarƙashin Shugaba Olusegun Obasanjo, gwamnatin tarayya ta janye shawarar, ta mayar da hedkwatar zuwa Ogbe-Ijoh. Wannan nasara ce ta farko a fili, ba ta tashin hankali ba, ta jajircewa.
A cikin shekarun da suka biyo baya, Tompolo ya fito a matsayin muryar jagoranci a gwagwarmayar Neja Delta. A matsayin wanda ya kafa ‘Moɓement for the Emancipation of the Niger Delta’ (MEND), ya ƙalubalanci tsarin tarayya wanda ke ƙwace biliyoyi daga ƙasar yankin amma ba ya mayar da komai. Saƙonsa yana da sauƙi amma mai ƙarfi ne: “Ba mu nemi yaki ba; muna neman adalci ne.”
Lokacin sauyi ya zo a shekarar 2009, lokacin da ya amince da Shirin Afuwa na Shugaban Ƙasa da marigayi Shugaba Umaru Musa Yar’Adua ya ƙaddamar. Duk da cin mutuncin wasu da shakku, ya ajiye makamai, yana ƙarfafa wasu su yi haka. Wannan ɗaya daga cikin ayyuka ya taimaka wajen kawo ƙarshen shekaru na tashin hankali da buɗe ƙofa ga gina zaman lafiya da tattaunawa mai tsari. Wannan shi ne farkon sauyi na mutum ɗaya da yankin baki ɗaya.
Daga Mai Ta Da Ƙayar Baya Zuwa Mai Tsara Ɗorewar Zaman Lafiya
Hannayen da da suka taɓa jagorantar jiragen yaƙi yanzu suna kula da wani sabon nau’in jiragen ruwa na ƙirƙira, samar da ayyukan yi, da kiyaye zaman lafiya. Ta hanyar Tantita Security Serɓices Nigeria Limited (TSSL), tare da haɗin gwiwa da Nigerian National Petroleum Company Limited (NNPCL), Tompolo ya zama mai tsaron muhimman kadarorin Nijeriya: bututun mai da tashoshin ruwan gabar teku.
Tsarin Tantita ya haɗa tsarin sa ido na zamani da bayanan sirri daga cikin al’umma, wanda hakan ya rage satar mai da aikin tace mai ba bisa ƙa’ida ba (“Kpo-fire”) a faɗin Niger Delta. Waɗannan ƙoƙari sun taimaka wajen ƙara yawan fitar da man fetur na kullum a Nijeriya, haɓaka kuɗaɗen shiga na gwamnati, da kuma dawo da amincewa da tsaron da al’umma ke jagoranta.
Amma ribar tattalin arziki rabin labari ne kawai. Fiye da mutane 3,000 daga cikin tsofaffin masu tayar da ƙayar baya da matasan yankin sun samu aikin doka mai ɗorewa ƙarƙashin kulawar Tantita.
Da yawa daga cikin waɗanda da suka ɗauki tawaye a matsayin hanya ɗaya ta samun muhimmanci, yanzu suna sanye da kayan aikin da ke da ma’ana. A cikin rafukan da da ake jin ƙarar bindigogi, yanzu ana jin ƙarar injinan jiragen ruwa masu ɗaukar ƙungiyoyin masu sa ido — hujja ce cewa zaman lafiya na iya kawo riba.
Faruwar Samun Nasarar Jin Ƙai
Nasarar da ta fi kowace girma ga Tompolo ita ce ta aikin jin ƙai cikin natsuwa.
Ta hannun Tompolo Education Foundation, yana ba da tallafin karatu da horas da malamai ga ɗaruruwan ɗalibai masu ƙaramin ƙarfi a faɗin yankin Neja Delta.
A watan Maris 2025, cibiyar ta ƙaddamar da shiria gina ƙwarewa ga ‘yan NYSC a yankin Warri domin ƙarfafa sababbin malamai da za su koyar a al’ummomin da ba su da wadatattun malamai.
Lokacin da Jami’ar Kiwon Ruwa ta Nijeriya (Nigeria Maritime Uniɓersity), Okerenkoko, ta gudanar da bikin yaye ɗalibai na farko, Tompolo ta hannun cibiyarsa ya ba da kayan ɗaki masu darajar Naira miliyan 30 don ƙarfafa muhalli na koyo.
Wannan ba taimako kawai ba ne, wani yanayi ne da ya tabbata: Tompolo ɗin da a da ake kira ɗan tawaye, yanzu shi ne ke zuba jari a cikin sabunta ilimin zamani.
Jin Ƙaunarsa Ta Kai Har Ga Fannin Kiwon Lafiya
A shekara ta 2012, ya biya kuɗin gyaran asibitin Okerenkoko guda ɗaya da darajar kuɗin suka kai naira miliyan 20.
Haka kuma, yayin ambaliyar ruwa ta shekarar 2022, Tompolo ya ba da kayan tallafi na darajar ta kai Naira miliyan 150 ga waɗanda ambaliyar ta shafa a jihohin Bayelsa da Delta, da Riɓers.
A gefe guda, Cibiyar Al’adu ta Izon (Izon Cultural Heritage Centre – ICHC) da Ƙungiyar Ayyukan Al’umma ta Izon (Izon Community Serɓice Ɓolunteers – ICSƁ) sun zama tushen farfaɗo da al’adu da ƙarfafa hidima ga al’umma.
Ta hanyar waɗannan ƙungiyoyi, Tompolo yana tunatar da matasan Ijaw cewa hidima ita ce mafi muhimmanci, kuma asalin bayyana kai ba wani tsohon abu ba ne tushen rayuwa ne mai ƙarfi da ci gaba.
Girmamawa Daga Jami’ar Maritime
Sauyin da ya samu daga kasancewa kwamandan ’yan tawaye zuwa zama mai daidaita ƙasa ya jawo masa yabo daga ko’ina.
A shekarar 2023, Jami’ar Maritime ta Nijeriya ta ba shi digirin girmamawa saboda gudunmawar da ya bayar wajen samar da zaman lafiya da ci gaba.
A shekara ta gaba kuma, Ƙungiyar Mutanen Ijaw ta Birtaniya da Ireland (Ijaw People’s Association – IPA) ta ba shi kyautar “Izon-Ebi Dou Keme” wato “Jagora mai kishin ci gaban al’ummar Ijaw.”
A yayin bikin ba da lambar girmamawar, Francis Akpanari, shugaban IPA, ya bayyana shi a matsayin “halattaccen ɗan Ijaw, wanda ya zama wata gada tsakanin rikici da haɗin kai.”
Amma wataƙila gaskatacciyar girmamawa ta fito ne daga al’umma kanta.
A cikin wata buɗaɗɗiyar wasika da ta bazu a kafafen sada zumunta, Oyinke Preye Tales, wata matashiya daga kogunan yankin, ta rubuta da motsin rai:
“Ba kawai shugaba ba ne kai, babban Cif ne kai, ƙarfi ne na yanayi, mai kare mutanen Ijaw da yankin Neja Delta.
Ka tsaya tsayin daka lokacin da da yawa suka durƙusa. Ka ɗauki nauyin fafutukar mu har da haɗarin rayuwa.
Saboda kai, ina tafiya ina ɗaga kai da alfahari.”
Wannan yabo ne na bazata daga sabon ƙarni wanda ba ta ganin yankin Neja Delta a matsayin wurin baƙin ciki da lalacewa, sai dai a matsayin wurin farfaɗo da sabuwar rayuwar abin da aka samu, a wani ɓangare, saboda zabin da ya yi da jagorancin da ya nuna.
Rayuwa Tasa, Manufa ta Jama’a
Duk da shahararsa da tasirinsa a siyasa, Tompolo har yanzu yana rayuwa cikin sauƙi da tawali’u. Yana zaune cikin natsuwa a Jihar Delta tare da matarsa Ɓictoria da ’yarsa Mary, yana guje wa nuna isa da shahara, yana fifita tunani da tunawa.
Masu kusanci da shi suna bayyana shi a matsayin mutum mai cike da natsuwa, wanda har yanzu yake ɗauke da raunukan yaƙin da ya shuɗe, amma yana samun warkewa ta hanyar zaman lafiya da ya taimakawa wajen gina al’umma.
A Wajen Mutanensa, Shi Ne Ibe-Ebidouwei Na Al’ummar Ijaw “Wanda Ke Kawo Alheri Ga Jama’a.”
A wajen Nijeriya kuma, shi hujja ce cewa sasantawa ba rauni ba ce, kuma cewa tuba da aka haɗa da manufa na iya zama babban arzikin ƙasa.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: yankin Neja Delta zaman lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Dauda Lawal: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba
Baya ga haka, sabon ginin ma’aikatar harkokin mata da ci gaban al’umma ta Jihar Zamfara da aka sake ginawa da kuma sabon ginin kwalejin fasaha da kimiyya na Jihar Zamfara (ZACAS) da aka gyara, sun yi matuƙar haskaka Gwamnatin Dauda Lawal.
Har ila yau, jihar ta samu gagarumin ci gaba wajen inganta fannin kiwon lafiya ta hanyar zuba jari, wajen gyarawa da inganta asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a faɗin jihar.
A ƙoƙarinsa na rage mace-macen mata masu juna biyu da mace-macen jarirai, an ɗauki ma’aikatan kiwon lafiya tare da horar da su da sayen magunguna da kayan aiki da ɓullo da ayyukan kula da lafiyar mata da ƙananan yara kyauta.
Sannan, an gyara asibitin ƙwararru na Yeriman Bakura tare da samar da kayan aiki na zamani. Haka kuma an gyara tare da samar da kayan aiki ga babban asibitin da ke Ƙaramar Hukumar Kauran Namoda a jihar. Babban asibitin da ke Kauran Namoda da sauran al’ummomin da ke makwabtaka da shi, an samar da kayan aiki don isar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya yadda ya kamata. Kazalika, an sanya na’urorin bincike, gadaje, injinan ECG, injin centrifuge, injinan gwaje-gwajen jini, na’urar tantance jini ta atomatik da sauran wasu kayan aiki.
Kazalika, an kuma inganta babban asibitin Nasarawar Burkullu da ke Ƙaramar Hukumar Bukkuyum. Bayan ayyukan kiwon lafiya da suka haɗa da na gaggawa, aikin tiyata, kula da lafiyar mata da yara, tsarin wurin keɓewa, wurin ajiyar gawa, ɗakunan tiyata na maza da mata, GOPD, ɗakin gwaje-gwaje, shagon magani, kula da mata masu juna biyu da kula da yar, duk an gina su. Sauran gyare-gyaren, sun haɗa da shingen gudanarwa, wuraren ma’aikata, masallatai da rijiyoyin burtsatse.
Haka kuma, a Ƙaramar Hukumar Maru, an gyara babban asibitin tare da samar da kayan aiki na zamani.
Gwamnan ya kuma kaƙƙamar da aikin sabunta birane, wanda ya kai ga gyara manyan tituna a jihar.
Dangane da batun tsaro kuwa, a shekarun baya-bayan nan, Zamfara ta ɗan samu jinkiri. A wannan lokaci na Gwamna Lawal, kashe-kashe da garkuwa da mutane ya ragu matuƙa a jihar. Hakan ya biyo bayan kafa jami’an tsaron da aka kafa a dukkanin kananan hukumomi 14 na Jihar Zamfara.
An horar da mutanen da aka zaɓo a tsanake, bisa cikakkiyar kulawar jami’an tsaron hukumar DSS, sannan suna yin aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro na yau da kullum, domin yaƙi da ‘yan fashi a jihar. A kwanakin baya ne gwamnan ya raba motocin aiki guda 140 da aka ware wa ƙungiyoyin tsaro daban-daban a faɗin jihar.
An haifi Dauda Lawal Dare, a ranar 2 ga Satumbar 1965, a Jihar Zamfara. Bayan kammala karatunsa na Firamare da Sakandare, ya halarci Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, inda ya yi digirinsa na farko a fannin Kimiyyar Siyasa. Ya kuma yi digirinsa na biyu (M.Sc) a fannin kimiyyar siyasa/Hukunce-hukuncen ƙasa da ƙasa duk a jami’ar. Ya ƙara da digirin-digirgir (PhD) a fannin harkokin kasuwanci a jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato.
Bayan kammala karatunsa na digiri na uku, ya yi kwasa-kwasai a Makarantar Kasuwanci ta Harɓard, Makarantar Kasuwanci ta Jami’ar Oɗford, Makarantar Tattalin Arziƙi ta Landan, Makarantar Kasuwancin Legas da sauransu.
Gwamnan ya yi aiki a matsayin jami’in ilimin siyasa tare da MAMSER, hukumar wayar da kan jama’a, don tabbatar da adalci da dogaro da kai a Nijeriya. A 1989, ya shiga Westeɗ Nigeria Limited a matsayin mataimakin babban manaja.
An naɗa shi a matsayin mataimakin ƙaramin jami’in shige da fice (immigration), a shekarar 1994, sannan ya zama babban jami’in hulɗa da jama’a a ofishin Jakadancin Nijeriya, Washington, DC, Amurka.
A shekarar 2003, ya koma bankin First Bank, a matsayin manajan hulɗa da jama’a, kuma a lokuta daban-daban ya kasance babban manaja a ofishin Abuja. A shekarar 2011, ya samu muƙamin mataimakin shugaban zartaswa, sashen gwamnati na Arewa na bankin na First Bank, bayan ya yi ayyuka da dama. A shekarar 2012, Dauda Lawal ya zama babban darakta a sashen gwamnati na Arewa, na First Bank.
Daga baya ya shiga siyasa ya kuma tsaya takarar Gwamnan Jihar Zamfara. A zaɓen fidda gwani na APC da aka gudanar a shekarar 2018, ya sha kaye a hannun Idris Shehu Mukhtar. A zaben Gwamnan Jihar Zamfara na 2023, ya tsaya takara; kuma ya yi nasara a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA