Leadership News Hausa:
2025-12-09@12:31:29 GMT

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

Published: 25th, October 2025 GMT

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

Lokacin da Etuh ya zama wanda ake maganarsa  musamman ma idan an taɓo maganar Takin zamani,  masana’antar ta kama hanyar lalacewa saboda ‘yan baran da sun mamaye ta, ga kuma cuwa-cuwa da ta yi wa wurin katutu, lamarin da ke sa ba a iya gane manoman gaskiya.

Duk da hakan ba ta sa Etuh ya yi ƙasa a gwiwa ba wajen haɗa kan da ya yi da gwamnatin tarayya, Etuh ya taimaka wa tsarawa da kuma gabatar da lamarin Takin zamani na Shugaban ƙasa Bola Tinubu (PFI),lamarin da ya kawo gaggarumin ci gaban aikin gona, domin kuwa an samu raguwar farashi,ya kuma samar da wata kafa inda manoma suke samun Takin zamanin kai tsaye.

Sakamakon haka ya sa yanzu an ƙara samun ci gaba, domin da farko ana da inji  1 ake amfani da shi a shekarar 2016, Nijeriya  yanzu tana da injuna fiye da 70 duk kuma mashin ɗaya yanzu akwai hanyar samar da ayyuka , yin takin,  da kuma bunƙasa ƙauyuka.

Kamfanin Etuh’s Mikap tare da tawagar FEPSAN  sun haɗa kansu wajen samar da Takin zamani fiye da buhuna miliyan 50  na takin zamani mai suna Kamfa ko kuma NPK  a ƙasa baki ɗaya, hakan ya sa an bar dogara da shigo da shi Takin daga ƙasashen waje, an kuma ceto Nijeriya daga amfani da biliyoyin Naira ta hanyar kuɗaɗen ƙasashen waje.

Taimakawa wajen yin takin zamani na gida

Hangen nesa irin na Etuh abin ya wuce maganar Takin zamani. Saboda yana son bunƙasa aikin noman ne daga ciki zuwa waje— daga lokacin shukawa zuwa har ya kai ga nuna a yi girbi a kawo gida ko kuma zuma kasuwa.

Ta hanyar Kamfanin Mikap Nijeriya, ya zuba jari na yadda ake yin Takin zamani da inji,  yadda za a kai shi gida bayan an girbe,  kai shi wurin ajiya, tabbatar da cewa an bar noma ta  kai ga shigar kowane ɓangare na tattalin  arziki.

Ganin yadda ya maida hankali ya sa gwamnatocin Jihohi suka haɗa kai da shi, ƙungiyoyin tsimi da tanaji, da kuma  ƙananan Bankuna da suke harkar kuɗaɗe, suna ba da dama ta bayar da bashi ga ƙananan manoma waɗanda suka rasa waɗanda za su ba su bashi.

A kowace Jiha inda ake yin wannan tsarin, rayuwar jama’a ta inganta, matasa sun samu aikin yi, yayin da mata kuma suka samu madafar da za su tsaya da ƙafafaunsu.

Yadda ake amfana da Thomas Etuh

An raba buhunan Takin Zamani miliyan 50 a faɗin tarayyar Nijeriya

An gyara injinan yin Taki fiye da Injina 70 da kuma sake  duba wasu, inda dubban manoma suka amfana da irin taimakon kai tsaye.

An samu dubban ayyukan yi sanadiyar lamarin na Takin Zamani.

An hana kashe bilyoyin kuɗaɗen ƙasar wajen da za a yi amfani da su saboda shigo da Takin da ake yi cikin gida Nijeriya wanda ake yi ta hanyar amfani da kayan gida.

Kowane ya samu wakilci ba kawai ya cancanci abin da ya samu ba, sai dai kuma babban jin daɗi— an samu ƙaruwar jin daɗin ‘yan Nijeriya.

Daga tsarin Takin  Zamani na Gida Zuwa Ga Tsari Ko Manufar Nijeriya

A matsayin shi na Shugaban masu yin Takin Zamani da raba shi na ƙasa (FEPSAN), Etuh shi ya kasance murya wanda ya damu da yadda ɓangaren yake.

Ya jagoranci maganar samar da kayan da za a haɗa wajen yin Takin Zamani, domin tabbatar da cewar masana’antun kamar su limestone, urea, da phosphate sun zama sune abubuwan da za ‘a riƙa yin amfani da su wajen yin shi Takin Zamanin.

Haka nan ma shi ne jagora na kula da ingancin shi Takin Zamanin yin hakan kuma an samu maganin waɗanda suke shigo da Takin Zamani da baya da inganci. Manoma yanzu suna samun Takin Zamani wanda ya dace da yanayin da ƙasar gonarsu take da kuma irin amfanin gonar  da za su shuka— domin kimiyya ta sa an bar yin cece- kuce ana amfani da zarihi ne.

Ta hanyar tattaunawar da yake yi da masu aiwatar da tsare tsare, Etuh ya taimaka wajen kawo gyara kan lamarin daya shafi Takin Zamani na ƙasa yadda za a inganta shi, wanda yanzu ɗauki matakin ya sa ana amfani da irin matakin da aka yi amfani da shi a nahiyar Afirka ta kudu da Sahara.

Abin ya wuce kasuwanci har da taimaka wa al’umma

Yadda Etuh yake manufa da sha’awa ta taimakawa al’umma domin su samu ci gaba. Ta hanyar gidauniyar Thomas Etuh, ya taimaka wa ɓangaren ilimi, lafiya, da kuma tallafa wa matasa a Jihohin  Kogi, Benuwe, da kuma Nasarawa.

Ya ba da tallafin ga ɗalibai ‘yan asalin Jihar, da kuma ba su horo ta ɓangaren aikin gona, da kuma ba da tallafi domin ƙananan masana’antu inda za a riƙa sarrafa abin da aka noma saboda ƙungiyoyin mata.

A shekarar 2024, gidauniyar ta ƙaddamar da tsarin Green Rural Initiatiɓe, wanda  ke da sabbin manoma — 5,000  kowace shekara. Tsarin yana nuna duk ƙaryar ci gaban Birane da ƙauyuka suke taƙama.

Shugaba mai niyyar taimako

Ya san yadda zai ja hankalin mutane ta hanyar iya maganarsa, an  san Etuh kan yadda yake shirye- shiryen shi ,  ga shi da son taimakon al’umma da kuma haɗin kai.

Abokan harkokinsa sun shi mutum ne wanda Allah ya sa ma shi tausayi na taimakawa, sai dai kuma duk wani , matakin da zai ɗauka sai ya yi tunani tukuna—ɗa bi;un nasa su sukka sa al’umma suka amince da shi har ma tare da gwamnati.

Ya yi karatunsa a Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya, ya kuma samu horo kan tsare-tsare da manufofi na manyan jami’ai a nan cikin gida da kuma waje, Etuh ya kawo ƙwararru ƙwarai da gaske zuwa ga ɓangaren waɗanda wani lokaci ba a ɗaukesu da muhimmanci ba. Manyan jami’an da yake yi aiki da su sun kwashe shekaru masu yawa a masana’antu, harkar kuɗaɗe da kuma ci gaba, amma duk da hakan babban abin da ya fi damuwa da sa shi ne ƙasar da ake yin noman a kanta, saboda ita ce babbar ma’aikatar dukiya.

Yadda ya samu jinjina daga gida da waje

A ƙarƙashin jagorancin Etuh, masana’antar takin zamani ta Nijeriya ta samu gagarumin nasara a nahiyar. Ƙungiyoyin yankin kamar irinsu Ƙungiyar Haɗin Gwiwar Takin Zamani da Kasuwancin Noma na Afirka (AFAP) da Shirin Haɓaka Noma a Afirka (AGRA) sun amince da haɗin gwiwa da Nijeriya a harkar noma da kamfanoni masu zaman kansu suka jagoranta.

Ya sama lambobin yabo masu tarin yawa a harkokin kasuwanci da samar da kayayyaki na ƙasa da ƙasa da kuma ɓangaren shugabancin noma, amma Etuh babbar bajintarsa ta fi shahara lokacin girɓin amfanin gona.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3) October 25, 2025 Manyan Labarai Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba October 25, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar October 24, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Sakkwato (ASUU-SSU), ta zargi Mataimakin Shugaban Jami’ar (Vice-Chancellor) da kin bin umarnin Gwamnan Jihar Sakkwato game da sauke Bursar da ya kai lokacin ritaya.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a Sakkwato a ranar Litinin, 8 ga Disamba 2025, ƙungiyar ta ce Gwamna Dr. Ahmed Aliyu Sakkwato, wanda shi ne Visitor na Jami’ar, ya amince da buƙatarsu na tabbatar da bin dokokin Jami’ar ta hanyar amincewa da ritayar Bursar ɗin.

ASUU-SSU ta bayyana cewa Ofishin Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar Sakkwato ya aika da takardar umarni mai lamba HS/ADM/101/VOL-1, ɗauke da kwanan wata 18 ga Nuwamba 2025, wadda ta umurci Bursar ya miƙa ragamar ofis ga jami’in da ya fi kowa girma a sashen Bursary, har sai an naɗa sabon Bursar bisa tanadin dokar Jami’ar Jihar Sakkwato ta 2009.

Sai dai ƙungiyar ta ce kusan wata guda ke nan VC ɗin bai aiwatar da umarnin ba.

Shugaban reshen ASUU-SSU, Kwamared Bello Musa, ya bayyana cewa sun rubuta wa VC takardar tunatarwa da wata takarda ta biyu, amma ba su samu amsa ba.

Haka kuma, sun gudanar da taro biyu da shi, amma ya dage cewa akwai wata amincewa da Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi ta jihar ta bayar a 2024 game da matsayin Bursar.

Sai dai ASUU ta ce wannan hujja “ba ta da tushe”, domin sabon umarnin Gwamna “ya fi ƙarfi kuma ya shafe duk wani tsohon matsayi”, musamman ma ganin cewa Bursar ya kai lokacin ritaya tun 3 ga Oktoba 2024.

A cewarta, Ma’aikatar Kula Da Ma’aikata ta riga ta aika masa da takardar ritaya ta hannun Ma’aikatar Kudi ta jihar.

Ƙungiyar ta ce ci gaba da bari tsohon ma’aikaci ya rattaɓa hannu kan muhimman takardun Jami’a “na karya doka, kuma na tauye ikon Jami’a (University Autonomy).”

ASUU-SSU ta yaba wa Gwamnan jihar bisa “ƙarin nuna biyayya ga doka da buɗe ƙofar sauraron ƙorafe-ƙorafe”, tare da buƙatar ya tabbatar da cewa ba a katse hanyoyin isar da sahihan koke-koke zuwa gare shi ba.

Ƙungiyar ta ce zanga-zangar lumana da ta gudanar a Jami’ar na nufin matsa wa VC lamba ya aiwatar da umarnin Gwamna ba tare da ɓata lokaci ba, domin tabbatar da zaman lafiya da daidaiton aiki.

Ta kuma sha alwashin ɗaukar “mataki mafi tsauri” idan ba a aiwatar da umarnin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba
  • Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa
  • Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan  Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko  Da  ‘Yan Ta’adda
  • ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
  • Kasashen Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Duk Wani Rikici
  • Iran Da Kasashen Afrika Sun Daura Dammarar Karfafa Alakar Kimiyya Tsakaninsu
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a Sakkwato
  • Tawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166
  • ’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno