Leadership News Hausa:
2025-10-25@14:27:44 GMT

Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

Published: 25th, October 2025 GMT

Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau I. Jibrin, ya bayyana cewa su na nazarin dokoki guda 69 da kuma buƙatun ƙirƙirar jihohi 55 da kuma ƙudirin ƙirƙirar ƙananan hukumomi 278 bisa ga tsarin kundin mulkin 1999.

Barau, wanda shi ne shugaban Kwamitin Bita na Tsarin Mulki a majalisar dattawa, ya bayyana hakan ne a taron haɗin gwuiwa da kwamitocin majalisar dattawa da kwamitocin majalisar wakilai kan gyare-gyaren dokokin tsarin mulki da suka gudanar a Lagos.

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu Firimiyar Nijeriya: Barau FC Ta Samu Nasarar Farko A Tarihinta

Ya jaddada cewa an dauki lokaci mai tsawo wajen tattaunawa da al’umma da masu ruwa-da-tsaki da ƙungiyoyi daban-daban, domin kawo waɗannan ƙuduri a gaban majalisar.

Ya kuma bayyana burin majalisar cewa za ta miƙa kashi na farko na gyare-gyaren tsarin mulki ga majalisun jihohi kafin ƙarshen shekarar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025 Gbenga Olu Komolafe October 25, 2025 Manyan Labarai Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025 October 25, 2025 Manyan Labarai Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3) October 25, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara Ta Ƙone Fiye da Rumbuna 500 a Kasuwar Kano

Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta tabbatar da cewa gobara ta lalata rumfuna 529 daga cikin rumfuna na wucin gadi a Kasuwar Shuwaki da ke ƙaramar hukumar Gari, Jihar Kano.

Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta jihar, Alhaji Saminu Abdullahi, ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai a Kano.

A cewarsa, hukumar ta samu kiran gaggawa misalin ƙarfe 3:25 na rana daga Abdulmalik Muhammad na ofishin kashe gobara na Gari, yana sanar da aukuwar gobara a kasuwar.

Ya bayyana cewa, da zarar sun samu bayanin, hukumar ta aika jami’ai da motocin kashe gobara zuwa wurin domin kashe wutar tare da hana ta yaduwa zuwa sauran sassan kasuwar.

Saminu ya ce yankin kasuwar yana da fadin kimanin kafa 3,000 da 2,500, kuma yana ɗauke da kusan rumfuna 1,000 na wucin gadi, inda rumfuna 529 suka ƙone ƙurmus.

Sai dai ya tabbatar cewa ba a rasa rai ba a wannan hatsari.

Ya danganta musabbabin gobarar da aikace-aikacen wasu mutane masu shaye-shaye da ke zaune a cikin kasuwar.

Mai magana da yawun hukumar ya shawarci jama’a da ’yan kasuwa da su kasance masu hankali da taka-tsantsan wajen amfani da wuta da abubuwan da ke iya kama da wuta, domin kauce wa irin wannan ibtila’i a nan gaba.

Khadijah Aliyu

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya faɗa wa ’yan Najeriya dalilin sauya hafsoshin tsaro — ADC
  • A Shirye Nake Na Kare Nasarar Da Na Samu A Zabe – Tchiroma Bakary
  • Matasa Dubu Ɗaya Za Su Samu Horon Fasahar Zamani A Nasarawa — Remi Tinubu
  • Gwamnatin Jihar Sokoto Ta Amince da Sauya Amfani da Naira Biliyan 526 a Kasafin Kuɗin 2025
  • Gobara Ta Ƙone Fiye da Rumbuna 500 a Kasuwar Kano
  • Majalisar Tattalin Arziki Ta Amince da Shirin Gyara Cibiyoyin Horar da Jami’an Tsaro
  • Kwamishinan Ilimi Na Kano Ya Yi Kira Da A Karfafa Shugabancin Makarantu Domin Inganta Karatun Dalibai
  • Kamaru: Sai ranar Litinin Majalisar tsarin mulki za ta bayyana wanda ya lashe zaben shugaban kasa
  • Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa