Leadership News Hausa:
2025-06-14@14:23:39 GMT

Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho

Published: 21st, May 2025 GMT

Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho

Amma kuma kariyar ciniki ba za ta taimaka ga raya sana’o’i da masana’antu a duniya ba. Idan mun lura, a cikin shekaru 10 da suka wuce, yadda kasar Amurka ta dauki matakai na kare sana’o’in samar da karafa, a maimakon ya hana raguwar guraben ayyukan samar da karafa, sai ya haifar da karuwar kudaden da sana’o’i masu alaka suka kashe.

Haka al’amarin yake ma ta fannin samar da sassan na’urorin laturoni na Chips da fasahohin kirkirarriyar basira, domin rashin yin takara da hadin gwiwa da sauran kasashe ba zai haifar da da mai ido ba, illa koma baya da illoli ga sana’o’i masu alaka.

A bangaren kasar Sin kuma, yadda kasar Amurka ke yi mata kafar ungulu don dakile ci gabanta, ya sa wa kamfanonin kasar kaimin gaggauta kirkire-kirkire, don neman tsayawa da kafafuwansu a fannin kimiyya. Idan ba mu manta ba, a farkon bana, kamfanin DeepSeek mai nazarin fasahar kirkirarriyar basira na kasar Sin ya fitar da tsarin R1 da ingancin aikinsa ya kai matsayin na sauran tsarukan AI masu matsayin koli na duniya. Har ma jaridar Financial Times ta kasar Burtaniya ta yi sharhin cewa, babban kuskure ne ga Amurka yadda take neman dakile ci gaban kasar Sin. Abubuwan da suka wakana a tarihi sun shaida mana cewa, ci gaban fasahohi su kan samu ne daga rikici da takara da juna, a maimakon zaman walwala. Ita kuma tsohuwar mukaddashiyar mai mataimaka wa sakataren harkokin wajen kasar Amurka, Susan Thornton, ta yi nuni da cewa, matakan kayyadewa da Amurka ta dauka, a hakika sun yi matukar samar da kuzari ga kasar Sin ta fannin kirkire-kirkire, inda Deepseek ya shaida hakan. Ta ce, “ba zai yiwu Amurka ita kadai ta mallaki fasahar kirkirarriyar basira ba, kamata ya yi gwamnatin Amurka ta yi watsi da kariyar ciniki da ma kiyayya da take wa kasar Sin, kuma ta yi hadin gwiwa da kasar, don samar da alfanu ga dukkanin bil-Adama bisa fasahar kirkirarriyar basira.”

Ma iya cewa, Madam Susan Thornton mai idon basira ce game da bunkasar sana’o’i masu alaka da fasahar kirkirarriyar basira. Lallai kawo tarnaki ga wasu ba ya kara wa mai yin hakan sauri da kuzarin tafiya. Matakan da kasar Amurka ke dauka na neman dakile ci gaban kasar Sin, ba zai haifar da kome ba, illa su sa kasar ta Sin ta kara karfinta da gaggauta ci gabanta. Sabo da kamar yadda a kan ce, sara da sassaka ba ya hana gamji toho.

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Amurka

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila

Jami’in kungiyar Hamas ya bayyana cewa: Kakkausan martanin da Iran ta mayar ya tabbatar da cewa babu mai girman kai da ba zai fuskanci mayar da martani ba

Izzat al-Rishq mamba na ofishin siyasa na kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ya jaddada cewa: Kakkausan martanin da Iraniyawa suka mayar ya tabbatar da cewa; babu mai girman kai da ba zai fuskanci mayar da martani kan zaluncinsa ba, kuma babu wuce gona da iri ba tare da hukunci ba.

Izzat al-Rishq ya yi nuni da cewa: Tabbas makamai masu linzami da jiragen saman yaki marasa matuka ciki na Iran sun yi nasarar kai wa cikin tsakiyar haramtacciyar kasar Isra’ila, duk kuwa da kace-nacen da ake yi na girke na’urorin kakkabo makamai a haramtacciyar kasar Isra’ila musamman Iron Dome, Arrow da David’s Sling.

Al-Rashq ya kuma bayyana cewa: Tsarin tsaron haramtacciyar kasar Isra’ila ya gaza shawo kan hare-haren da Iran suka kai, kuma a halin yanzu gwamnatin mamayar Isra’ila tana fama da gobarar da ta kunna a tsakanin al’ummomin yankin. A karshe ya jaddada cewa: Sakon a bayyane yake: Duk wanda ya yi tsokana, to tantana kudarsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  • An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe
  • Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar
  • An Gudanar Da Taron Ministoci Masu Daidaita Ayyukan Da Aka Amince Yayin Taron FOCAC
  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Kaso Kusan 80% Sun Soki Musabbabin Barkewar Tarzoma A Amurka
  • Amurka da China sun cimma sabuwar yarjejeniyar kasuwanci
  • Birnin Los Angeles Na Amurka Ya Rikice Yadda Ake Dauki Ba Dadi Tsakanin Al’ummar Jihar Da Jami’an Tsaro