HausaTv:
2025-12-13@13:51:57 GMT

Baka’i: Za Mu Mayar Da Martani Akan Wasikar Trump Bayan Yin Nazari

Published: 17th, March 2025 GMT

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen jamhuriyar musulunci ta Iran Isma’ila Baka’i ya ce; Abinda ake watsawa a matsayin wasikar shugaban kasar Amurka shaci-fadi ne, domin har yanzu, mu ba mu watsa abinda ta kunsa ba.”

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya kuma ce; Da akwai banbanci a tsakanin yadda Donald Trump yake Magana a fili da kuma abinda wasikar tasa ta kunsa.

Dr. Baka’i ya kuma kara da cewa; Bayan yin nazarin wasikar da abinda ta kunsa za mu bayar da jawabi.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya kore cewa ziyarar da ministan ma’aikatar tasu Abbas Arakci ya kai zuwa kasar Oman yana da alaka da bayar da jawabin wannan wasikar ta shugaban kasar Amurka.

Da yake mayar da jawabi akan harin da Amurka ta kai wa kasar Yemen, Dr. Baka’i ya ce abin takaici wannan ba shi ne karon farko da Amurkan ta kai wa Yemen hari ba, wanda shakka babu laifi ne kuma abin ayi Allawadai da shi ne.

Dr. Baka’i, ya  kuma yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da kuma kasashen musulmi da kungiyar kasashen ta musulmi da su dauki matakin gaggawa akan abinda yake faruwa.

Dangane da barazanar kai wa Iran hari, kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya ce; Duk wani wuce gona da iri akan Iran zai fuskanci mayar da martani mai tsanani ba tare da taraddudi ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ma aikatar harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Yi Tir Da Yanke Tallafin Da MDD Take Bawa Yan Gudun Hijiran Afganistan

Gwamnatin kasar Iran ta yi kakkausar suka ga kasashen duniya wadanda suka rage yawan kudaden da suke bayarwa don tallafawa yan gudun hijira daga kasar Afganisatan a cikin kasar Iran.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto jakadan kasar Iran a MDD Amir Saeed Iravani yana fadar haka a jawabinda ya gabatar a taron kwamitin tsaro na MDD dangane da kasar ta Afganistan a jiya Laraba.

Iravani ya kara da cewa a halin yanzun Iran tana ci gaba da daukar bakwncin yan gudun hijiran Afganisatan fiye da miliyon 6 wanda ya hada da da shi da shansu da karatun yayansu da kuma tallafin da gwamnatin kasar take bayarwa na gidajen zamansu da ruwa da wutan lanatarki. Wanda a halin yanzu tana kashe akalla dalar Amurka billion $1o don yin hakan.

Kafin haka dai kwamitin tsaro na majalisar ya tsaida shawarar rage kashe 65% na kudaden da take bawa kasar Iran dangane da yan gudun hijiran Afganistan fiye da miliyon 6 da suke zama a kasar a shekara mai zuwa wato 2026.

Iravani ya musanta zancen tsohon jakafan Amurka a Zalmay Khalilzad wanda ke cewa ai Iran ta kore mafi yawan yan gudun hijiran Afganisatan a kasar. Ya ce wadanda Iran ta kora sune wadanda suka  shiga kasar ba tare da takardun shaida ba. Wannan kuma an amince da shi a ko ina a duniya.  

Iravani ya bayyana cewa, wannan matakin ya sabawa al-kawalin da kasashen duniya suka dauka na daukan nauyin yan gudun hijira a duniya. Ba zasu bar nauyin a kan kasa guda ba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka December 11, 2025 Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan December 11, 2025 ECOWAS ta bukaci waware batutuwa na siyasa ta hanyoyin lumana a yammacin Afirka December 11, 2025 Reuters: Amurka na matsa lamba kan kotun ICC don janye bincike kan yakin  Gaza da Afghanistan December 11, 2025 Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila December 11, 2025 Sakamkon Jin Ra’ayi: Yawancin Amurkawa na adawa da kai hari kan Venezuela December 11, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Kasashen Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5  December 10, 2025 Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa December 10, 2025 Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD December 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Ilimi ta Jigawa Za Ta Kashe Naira Biliyan 18 a 2026
  • 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
  • Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare
  • Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan
  • Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut
  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • Iran Ta Yi Tir Da Yanke Tallafin Da MDD Take Bawa Yan Gudun Hijiran Afganistan