HausaTv:
2025-05-21@11:31:19 GMT

EU ta dage takunkumin da ta kakaba wa Syria

Published: 21st, May 2025 GMT

Bayan sanarwar ba-zata da Amurka ta yi a makon da ya gabata, Tarayyar Turai ta ce za ta dage takunkumin da ta kakaba wa Syria.

Ministocin harkokin waje da ke taro a Brussels ne suka yanke shawarar dage dukkan takunkumin tattalin arzikin kan Siriya.

“Muna son taimakawa al’ummar Siriya wajen sake gina sabuwar Siriya,” in ji jami’ar kula da harkokin wajen Tarayyar Turai Kaja Kalas.

Tarayyar Turai ta kuma yi alkawarin bayar da Yuro biliyan biyu da rabi domin sake gina kasar.

Matakin dage wannan takunkumin da aka kakabawa gwamnatin Bashar al-Assad tun daga shekara ta 2011, zai bada damar sakin kadarorin kasar da har yanzu ke daskare, sannan kuma zai baiwa hukumomin kasar damar neman zuba jarin da suke bukata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tehran ta yi kakkausar suka kan tsare Iraniyawa a Birtaniya

Iran ta gayyaci mai kula da harkokin kasar Birtaniya a birnin Tehran, biyo bayan tsare wasu ‘yan kasarta da dama ba bisa ka’ida ba a kasar.

Shugaban bangaren kula da sashen yammacin turai a ma’aikatar harkokin wajen kasar ya yi kakkausar suka da nuna adawa da matakin na gwamnatin Birtaniyya, da kuma zarge-zargen da ba su dace ba da ake yi wa Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

Jami’in ya ce tsare ‘yan kasar Iran ya sabawa ka’idoji da dokokin kasa da kasa da kuma hakkokin bil’adama da aka amince da su, saboda an tuhume su ba tare da wata hujja ba.

Ya kara da cewa ‘yan kasar Iran da ake tsare da su, an kuma hana su harkokin ofishin jakadanci da kuma ba su kariya…

Jami’in na Iran ya jaddada cewa gwamnatin Birtaniyya ce ke da cikakken alhakin irin wadannan ayyuka, wadanda ake ganin suna da alaka da siyasa domin matsin lamba kan Iran.

A ranar Asabar an kama wasu mutane hudu ‘yan kasar Iran, kuma An tsare su ne a karkashin dokar ta’addanci, kamar yadda kafafen yada labaran Burtaniya suka ruwaito.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sakataren Harkokin Wajen Amurka Ya Ce; Gwamnatin Siriya Zata Iya Rugujewa Cikin ‘Yan Makonni
  • Fransa Ta Kira Yi Kasashen Turai Da Sake Bitar Alakarsu Da “Isra’ila”
  • Wasu Shugabannin Turai Sun Yi Barazanar Ladabtar Da Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Tattaunawar Iran da Amurka na inganta zaman lafiya a yankin : Araghchi
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Kasarsa Ta Jajirce Kan Harkokin Diflomasiyya Domin Kare Hakkokinta   
  • Iran : zamu ci gaba da inganta uranium ko da yarjejeniya ko babu
  • Taron Tehran ya bukaci tattaunawa cikin gaggawa kan kalubalen yankin  
  • Tehran ta yi kakkausar suka kan tsare Iraniyawa a Birtaniya
  • Kasar Sin Ta Samu Bunkasar Masana’antar Harkokin Tauraron Dan Adam A Shekarar 2024