HausaTv:
2025-07-05@19:05:17 GMT

EU ta dage takunkumin da ta kakaba wa Syria

Published: 21st, May 2025 GMT

Bayan sanarwar ba-zata da Amurka ta yi a makon da ya gabata, Tarayyar Turai ta ce za ta dage takunkumin da ta kakaba wa Syria.

Ministocin harkokin waje da ke taro a Brussels ne suka yanke shawarar dage dukkan takunkumin tattalin arzikin kan Siriya.

“Muna son taimakawa al’ummar Siriya wajen sake gina sabuwar Siriya,” in ji jami’ar kula da harkokin wajen Tarayyar Turai Kaja Kalas.

Tarayyar Turai ta kuma yi alkawarin bayar da Yuro biliyan biyu da rabi domin sake gina kasar.

Matakin dage wannan takunkumin da aka kakabawa gwamnatin Bashar al-Assad tun daga shekara ta 2011, zai bada damar sakin kadarorin kasar da har yanzu ke daskare, sannan kuma zai baiwa hukumomin kasar damar neman zuba jarin da suke bukata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Sake Aiwatar Da Kisan Kare Dangi Kan ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa

Sojojin mamayar Isra’ila sun kai munanan hare-hare kan Falasdinawa da suka rasa gidajensu da fama da masifar yunwa, lamarin da ya yi sanadiyar shahadan mutane da dama

Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila tana ci gaba da aiwatar da kisan kiyashi kan ‘yan gudun hijira da kuma wadanda ke jiran agaji a zirin Gaza, inda a daren jiya zuwa safiyar Alhamis, hare-haren wuce gona da irinsu suka yi sanadiyar shahadan Falasdinawa da dama, tare da jikkata wasu baya ga bacewar wai adadi mai yaw ana mutane a karkashin baraguzan gine-gine.

Asibitin Al-Shifa ya sanar da shahadan fararen hula 11 da suka hada da yara da mata a wani sabon kisan kiyashi da sojojin mamayar Isra’ila suka aikata ta hanyar kai hare-haren bama-bamai kan makarantar Mustafa Hafez da ke matsayin mafaka ga ‘yan gudun hijira a yammacin birnin Gaza.

Sannan a wani kisan kiyashi kuma, fararen hula 13 da suka hada da mata da kananan yara ne suka yi shahada a lokacin da jiragen yakin mamayar Isra’ila suka kai hare-hare kan wani tanti da ‘yan uwa Abu Asi suka yi gudun hijira ciki, kusa da masallacin Al-Aqqad da ke unguwar Mawasi a Khan Yunis. Wasu da dama kuma suka jikkata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu
  • Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
  • In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba
  • Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
  • Aragchi Ya Musanta Zargin Da Jamus Take Watsawa Dangane sa Shirin Nukliyar Kasar
  • Rasha ta amince da gwamnatin Taliban a Afghanistan
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Harin Kan Cibiyar Makamashin Nukiliya Cin Amanar Diflomasiyya Ce
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Sake Aiwatar Da Kisan Kare Dangi Kan ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa
  • Kalibof Yace: Iran Zata Maida Martani Mai Tsanani Kan HKI Idan Ta Sake Bude Yaki da Iran
  •  Arakci Ya Mayar Wa Da Jami’ar Harkokin Wajen ” EU” Martani