Leadership News Hausa:
2025-11-02@21:33:38 GMT

Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata

Published: 6th, July 2025 GMT

Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata

 

Rukunin farko: Morocco da Zambiya da Senegal da kuma Jamhuriyar Congo

Rukuni na biyu: Nijeriya da Tunisia da Algeria da kuma Botswana.

Rukuni na uku: Afirka ta Kudu da Ghana da Mali da kuma Tanzania.

Bayan karawar bude labulen gasar, akalla za a rika buga wasanni bibiyu kowacce rana a fafatawar cikin rukuni har zuwa ranar Litinin 14 ga watan Yuli.

Sannan a lokacin wasannin cikin rukuni za ake buga su daga 13:00 da 16:00 da kuma19:00 daidai da agogon GMT. Za a fara karawar zagaye na biyu daga ranar Juma’a 18 ga watan Yuli.

Shekara ukun da ta gabata, Morocco ta gudanar da gasar cin kofin Afirka ta mata, kuma filaye ukun da ta yi amfani da su, ba bu su daga cikin wadanda za su karbi bakuncin gasar bana. Kasar dake Arewacin Afirka na ci gaba da yin tsare-tsare da gyare-gyare, wadda za ta karbi bakuncin wasan cin kofin Afirka na maza da yin hadakar gasar cin kofin duniya da za a buga a 2030.

 

Za A Yi Amfani Da Filayen Wasa Shida A Birane Biyar Har Da Biyu A

Casablanca:

Olympic Stadium a Birnin Rabat (Mai cin ‘yan kallo 21,000)

El Bachir Stadium a Birnin Mohammedia (Mai cin ‘yan kallo 15,000)

Larbi Zaouli Stadium a Birnin Casablanca (Mai cin ‘yan kallo 30,000)

Pere Jego Stadium a Birnin Casablanca (Mai cin ‘yan kallo 10,000)

Honneur Stadium a Birnin Oujda (Mai cin ‘yan kallo 19,800)

Berkane Stadium a Birnin Berkane (Mai cin ‘yan kallo 15,000

Daga kasashe 12 da za su buga gasar cin kofin Afirka a Morocco, NIjeriya ce da Afirka ta Kudu ta taba daukar kofin. Super Falcons za ta fafata a wasannin karkashin koci, Justin Maduguwu. Chiamaka Nnadozie daga NIjeriya ita ce ta lashe kyautar fitatciyar mai tsaron raga a Afirka karo biyu, yayin da Asisat Oshoala za ta buga wasannin da ta dunga yin fice a baya.

Mai horar wa Desiree Ellis za ta yi kokarin kare kofin da yake hannun Afirka ta kudu, wadda za ta buga karawar ba tare da Thembi Kgatlana, saboda wasu dalilai na kashin kai. Haka ‘yar wasan Afirka ta Kudu, Jermaine Seoposenwe tana taka rawar gani a Monterrey a Medico da Hilda Magaia, wadanda aka rabawa takalmin zinare a matakin kan gaba a cin kwallaye a WAFCON a 2022.

Morocco tana zuba hannun jari mai yawa a fannin kwallon kafa a ‘yan shekaru da yawa, amma har yanzu tawagarta ta mata ta kasa kwaikwayon ta maza da ta taba taka matakin farko a buga wasa a Afirka. Sai dai Atlas Lionesses tana da mai horar wa Jorge Bilda, wanda ya lashe kofin duniya da tawagar Sifaniya a 2023. Zambia ta kare a mataki na uku a gasar baya da aka yi, tana kuma tare da wadda ta yi fice a fannin buga

mata wasa a Afirka a shekara, Barbra Banda, wadda ba ta buga gasar 2022 ba.

Mai buga wasa a Orlando Pride tana kan ganiya, wadda take wasa tare da Racheal Kundananji, wadanda suna daga cikin ‘yan wasa hudun da aka saya mafi tsada a tarihi. Ita kuwa ‘yar kasar Swistzerland, Nora Hauptel za ta ja ragamar Ghana ne domin lashe gasar karon farko a tarihi.

Bayan Nijeriya da Afirka ta Kudu da suke da tarihin lashe gasar kofin Afirka, Ghana tana da kwarewar halartar wasannin da ta yi a 1998 da 2002 da kuma 2006.

 

Wasannin cikin rukuni

Asabar 5 ga watan Yuli

Rukunin farko: Morocco da Zambia – Ranar Lahadi 6 ga watan Yuli

Rukunin farko: Senegal da Ibory Coast, El Bachir Stadium, Mohammedia

(14:00)

Rukunin na biyu: Nijeriya da Tunisia, Larbi Zaouli Stadium, Casablanca (16:00)

Rukunin na biyu: Algeria bs Botswana, Pere Jego Stadium, Casablanca (19:00)

 

Ranar Litinin 7 ga watan Yuli

Rukunin na uku: Afirka ta Kudu da Ghana, Honneur Stadium, Oujda

(16:00)

 

Rukunin na uku: Mali da Tanzania, Berkane Stadium, Berkane (19:00)

Ranar Laraba 9 ga watan Yuli

Rukunin farko: Zambiya da Senegal, Mohammedia (16:00)

Rukunin farko: Jamhuriyar Congo da Morocco, Rabat (19:00)

 

Ranar Alhamis 10 ga watan Yuli

Rukunin na biyu: Botswana da Nijeriya, Larbi Zaouli Stadium, Casablanca (16:00)

Rukunin na biyu: Tunisia da Algeria, Pere Jego Stadium, Casablanca (19:00)

Ranar Juma’a 11 ga watan Yuli

Rukunin na uku: Ghana da Mali, Berkane (16:00)

Rukunin na uku: Tanzania da South Africa, Oujda (19:00)

Ranar Asabar 12 ga watan Yuli

Rukunin farko: Morocco da Senegal, Rabat (19:00)

Rukunin farko: Zambiya da Jamhuriyar Congo, Mohammedia (19:00)

 

Ranar Lahadi 13 ga watan Yuli

Rukunin na biyu: Nijeriya da Algeria, Larbi Zaouli Stadium, Casablanca (19:00)

Rukunin na biyu: Tunisia da Botswana, Pere Jego Stadium, Casablanca (19:00)

Ranar Litinin 14 ga watan Yuli

Rukunin na uku: Afirka ta Kudu da Mali, Oujda (19:00)

Rukunin na uku: Ghana da Tanzania, Berkane (19:00)

Zagayen kwata fainal a WAFCON 2024

 

Ranar Juma’a 18 ga watan Yuli

Kwata fainal na farko: Wadda ta yi ta daya a rukunin farko da ta farko a rukuni na uku ko wadda ta yi ta uku a rukuni na biyu, za su yi wasa a Rabat

Kwata fainal na biyu: Wadda ta yi ta farko a rukuni na biyu da wadda ta yi ta biyu a rukunin farko, za su kece raini a Larbi Zaouli Stadium a Casablanca.

 

Ranar Asabar 19 ga watan yuli

Kwata fainal na uku: Wadda ta yi ta farko a rukuni na uku da ta daya a rukunin farko ko wadda ta kare a mataki na uku a rukuni na biyu, za su kara a Oujda

Kwata fainal na hudu: Wadda ta yi ta biyu a rukuni na biyu da wadda ta kare a mataki na biyu a rukuni na uku, za su yi wasa a Berkane

 

Wasannin dab da karshe a WAFCON 2024

Wasan dab da karshe na farko: Wadda ta ci zagayen kwata fainal a wasan farko za ta fuskanci wadda ta yi nasara a zagayen kwata final karawa ta hudu, za su kara a birnin Rabat.

Wasan dab da karshe na biyu: Wadda ta lashe zagayen kwata fainal wasa na biyu da wadda ta yi nasara a karawar kwata fainal na uku, za su kece raini a Larbi Zaouli Stadium a Casablanca.

Wasan neman mataki na uku da na hudu

Ranar Juma’a 25 ga watan Yuli

Wadda ta yi rashin nasara a dab da karshen farko da wadda aka doke a zagayen dab da karshe wasa na biyu, za su fafata a Larbi Zaouli Stadium a birnin Casablanca.

Wasan karshe na WAFCON 2024

Ranar Asabar 26 ga watan Yuli

Wadda ta lashe wasan farko na dab da karshe da wadda ta yi nasara a dab

da karshe na biyu, inda za su fafata a Olympic Stadium a Birnin Rabat.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda

A cewar ta a cikin shekarar 2024 jihar Katsina kawai ta samu masu wannan cuta mutum 17 tare da guda biyu a karamar hukumar Danmusa a cikin wannan shekara

Haka kuma Hajiya Zulaihat Radda ya bada tabbacin cewa kowane yaro an tabbatar da ya amshi allurar Riga-kafin shan Inna

Ana jawabin wakilin asusun tallafawa yara na UNICEF na ofishin Kano, Rahama Mohammed Farah ta yabawa kokarin jihar Katsina na dawo da sabon yunkurin kawar cutar shan Inna a Nijeriya baki daya

Ya kuma bayyana cewa asusun kula da kananan yara na UNICEF Yana hadin gwiwa da gwamnatoci da hukumomi da masu ruwa da tsaki a kananan hukumomi domin ganin wajen fadakar da al’umma akan allurar Riga-kafin shan Inna a jihar Katsina.

Shima da yake jawabi shugaban hukumar lafiya a matakin farko ta Jihar Katsina Dakta Shansudeen Yahaya ya yi alkawarin cigaba da wayar da kan al’umma akan wannan cuta ta shan Inna da sauran cututtuka masu kashe yara a kananan hukumomi 34 na jihar Katsina

Wadanda suka shaida wannan bikin ranar ‘Polio’ ta duniya sun hada da hukumar lafiya ta WHO da kuma masu lalurar cutar shan Inna da wakilan asusun UNICEF da matan shugabannin kananan hukumomi 34 na jihar Katsina

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi October 31, 2025 Manyan Labarai Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai October 31, 2025 Manyan Labarai Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda