Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata
Published: 6th, July 2025 GMT
Rukunin farko: Morocco da Zambiya da Senegal da kuma Jamhuriyar Congo
Rukuni na biyu: Nijeriya da Tunisia da Algeria da kuma Botswana.
Rukuni na uku: Afirka ta Kudu da Ghana da Mali da kuma Tanzania.
Bayan karawar bude labulen gasar, akalla za a rika buga wasanni bibiyu kowacce rana a fafatawar cikin rukuni har zuwa ranar Litinin 14 ga watan Yuli.
Shekara ukun da ta gabata, Morocco ta gudanar da gasar cin kofin Afirka ta mata, kuma filaye ukun da ta yi amfani da su, ba bu su daga cikin wadanda za su karbi bakuncin gasar bana. Kasar dake Arewacin Afirka na ci gaba da yin tsare-tsare da gyare-gyare, wadda za ta karbi bakuncin wasan cin kofin Afirka na maza da yin hadakar gasar cin kofin duniya da za a buga a 2030.
Za A Yi Amfani Da Filayen Wasa Shida A Birane Biyar Har Da Biyu A
Casablanca:
Olympic Stadium a Birnin Rabat (Mai cin ‘yan kallo 21,000)
El Bachir Stadium a Birnin Mohammedia (Mai cin ‘yan kallo 15,000)
Larbi Zaouli Stadium a Birnin Casablanca (Mai cin ‘yan kallo 30,000)
Pere Jego Stadium a Birnin Casablanca (Mai cin ‘yan kallo 10,000)
Honneur Stadium a Birnin Oujda (Mai cin ‘yan kallo 19,800)
Berkane Stadium a Birnin Berkane (Mai cin ‘yan kallo 15,000
Daga kasashe 12 da za su buga gasar cin kofin Afirka a Morocco, NIjeriya ce da Afirka ta Kudu ta taba daukar kofin. Super Falcons za ta fafata a wasannin karkashin koci, Justin Maduguwu. Chiamaka Nnadozie daga NIjeriya ita ce ta lashe kyautar fitatciyar mai tsaron raga a Afirka karo biyu, yayin da Asisat Oshoala za ta buga wasannin da ta dunga yin fice a baya.
Mai horar wa Desiree Ellis za ta yi kokarin kare kofin da yake hannun Afirka ta kudu, wadda za ta buga karawar ba tare da Thembi Kgatlana, saboda wasu dalilai na kashin kai. Haka ‘yar wasan Afirka ta Kudu, Jermaine Seoposenwe tana taka rawar gani a Monterrey a Medico da Hilda Magaia, wadanda aka rabawa takalmin zinare a matakin kan gaba a cin kwallaye a WAFCON a 2022.
Morocco tana zuba hannun jari mai yawa a fannin kwallon kafa a ‘yan shekaru da yawa, amma har yanzu tawagarta ta mata ta kasa kwaikwayon ta maza da ta taba taka matakin farko a buga wasa a Afirka. Sai dai Atlas Lionesses tana da mai horar wa Jorge Bilda, wanda ya lashe kofin duniya da tawagar Sifaniya a 2023. Zambia ta kare a mataki na uku a gasar baya da aka yi, tana kuma tare da wadda ta yi fice a fannin buga
mata wasa a Afirka a shekara, Barbra Banda, wadda ba ta buga gasar 2022 ba.
Mai buga wasa a Orlando Pride tana kan ganiya, wadda take wasa tare da Racheal Kundananji, wadanda suna daga cikin ‘yan wasa hudun da aka saya mafi tsada a tarihi. Ita kuwa ‘yar kasar Swistzerland, Nora Hauptel za ta ja ragamar Ghana ne domin lashe gasar karon farko a tarihi.
Bayan Nijeriya da Afirka ta Kudu da suke da tarihin lashe gasar kofin Afirka, Ghana tana da kwarewar halartar wasannin da ta yi a 1998 da 2002 da kuma 2006.
Wasannin cikin rukuni
Asabar 5 ga watan Yuli
Rukunin farko: Morocco da Zambia – Ranar Lahadi 6 ga watan Yuli
Rukunin farko: Senegal da Ibory Coast, El Bachir Stadium, Mohammedia
(14:00)
Rukunin na biyu: Nijeriya da Tunisia, Larbi Zaouli Stadium, Casablanca (16:00)
Rukunin na biyu: Algeria bs Botswana, Pere Jego Stadium, Casablanca (19:00)
Ranar Litinin 7 ga watan Yuli
Rukunin na uku: Afirka ta Kudu da Ghana, Honneur Stadium, Oujda
(16:00)
Rukunin na uku: Mali da Tanzania, Berkane Stadium, Berkane (19:00)
Ranar Laraba 9 ga watan Yuli
Rukunin farko: Zambiya da Senegal, Mohammedia (16:00)
Rukunin farko: Jamhuriyar Congo da Morocco, Rabat (19:00)
Ranar Alhamis 10 ga watan Yuli
Rukunin na biyu: Botswana da Nijeriya, Larbi Zaouli Stadium, Casablanca (16:00)
Rukunin na biyu: Tunisia da Algeria, Pere Jego Stadium, Casablanca (19:00)
Ranar Juma’a 11 ga watan Yuli
Rukunin na uku: Ghana da Mali, Berkane (16:00)
Rukunin na uku: Tanzania da South Africa, Oujda (19:00)
Ranar Asabar 12 ga watan Yuli
Rukunin farko: Morocco da Senegal, Rabat (19:00)
Rukunin farko: Zambiya da Jamhuriyar Congo, Mohammedia (19:00)
Ranar Lahadi 13 ga watan Yuli
Rukunin na biyu: Nijeriya da Algeria, Larbi Zaouli Stadium, Casablanca (19:00)
Rukunin na biyu: Tunisia da Botswana, Pere Jego Stadium, Casablanca (19:00)
Ranar Litinin 14 ga watan Yuli
Rukunin na uku: Afirka ta Kudu da Mali, Oujda (19:00)
Rukunin na uku: Ghana da Tanzania, Berkane (19:00)
Zagayen kwata fainal a WAFCON 2024
Ranar Juma’a 18 ga watan Yuli
Kwata fainal na farko: Wadda ta yi ta daya a rukunin farko da ta farko a rukuni na uku ko wadda ta yi ta uku a rukuni na biyu, za su yi wasa a Rabat
Kwata fainal na biyu: Wadda ta yi ta farko a rukuni na biyu da wadda ta yi ta biyu a rukunin farko, za su kece raini a Larbi Zaouli Stadium a Casablanca.
Ranar Asabar 19 ga watan yuli
Kwata fainal na uku: Wadda ta yi ta farko a rukuni na uku da ta daya a rukunin farko ko wadda ta kare a mataki na uku a rukuni na biyu, za su kara a Oujda
Kwata fainal na hudu: Wadda ta yi ta biyu a rukuni na biyu da wadda ta kare a mataki na biyu a rukuni na uku, za su yi wasa a Berkane
Wasannin dab da karshe a WAFCON 2024
Wasan dab da karshe na farko: Wadda ta ci zagayen kwata fainal a wasan farko za ta fuskanci wadda ta yi nasara a zagayen kwata final karawa ta hudu, za su kara a birnin Rabat.
Wasan dab da karshe na biyu: Wadda ta lashe zagayen kwata fainal wasa na biyu da wadda ta yi nasara a karawar kwata fainal na uku, za su kece raini a Larbi Zaouli Stadium a Casablanca.
Wasan neman mataki na uku da na hudu
Ranar Juma’a 25 ga watan Yuli
Wadda ta yi rashin nasara a dab da karshen farko da wadda aka doke a zagayen dab da karshe wasa na biyu, za su fafata a Larbi Zaouli Stadium a birnin Casablanca.
Wasan karshe na WAFCON 2024
Ranar Asabar 26 ga watan Yuli
Wadda ta lashe wasan farko na dab da karshe da wadda ta yi nasara a dab
da karshe na biyu, inda za su fafata a Olympic Stadium a Birnin Rabat.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Baltasar: Mutumin da ya fitar da bidiyon lalatarsa da mata sama da 400 ya gurfana a kotu
Baltasar Engonga Ebang, mutumin nan dan kasar Equatorial Guinea da a bara ya saki bidiyon lalatarsa da mata sama da 400 na fuskantar shari’a a kotu kan badakalar kudade.
Baltasar, wanda tsohon Shugaban Hukumar Yaki da Rashawa ta kasar Equatorial Guinea ne dai an gurfanar da shi a gaban kotu ne bisa zargin karkatar da kudade a karkashin Ma’aikatar Kudin kasar.
Masu shigar da kara na neman a yanke masa hukuncin daurin shekara 18 a kurkuru sannan a umarce shi ya dawo da wasu kudaden masu yawa.
’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar TIinubu – Amaechi Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin motaAna dai zarginsa ne da almundahana, azurta kai da kuma rub-da-ciki a kan dukiyar al’umma lokacin da yake rike da mukamin hukumar.
Lauyoyi masu shigar da kara na zargin Baltasar da yin babakere a kan kudi har sama da CFA biliyan daya, kwatankwacin sama da Naira biliyan biyu da rabi.
Bugu da kari, lauyoyin na kuma son a yanke masa hukuncin shekara takwas kan laifin almundahana, shekara hudu da wata biyar kan laifin azurta kai, sai kuma shekara shida kan laifin cin amanar ofishinsa.
Lauyoyin sun kuma bukaci kotun ta ci Baltasar tarar CFA miliyan 910 sannan a haramta masa rike kowanne irin ofishin gwamanti na tsawon lokacin da zai shafe a dauren.
To sai dai lauyoyin wanda ake karar sun yi fatali da dukkan laifukan da ake zargin wanda suke karewa da aikatawa da ma sauran wadanda ake zargin, inda suka ce bas u da tushe.
A watan Disambar bara ne dai bidiyoyin Baltasar na lalata da mata sama da 400 suka cika shafukan sada zumunta. Daga cikin matan da aka gan shi yana lalata da su har da matan ministotin kasar.