Aminiya:
2025-10-19@02:50:50 GMT

Ana zargin wa da ƙani da yi wa almajiri yankan rago a Adamawa

Published: 17th, March 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Adamawa ta cafke wani ƙani da yayansa — Aliyu Abdulmalik da Ibrahim Abdulmalik — kan zargin yanke kan wani almajiri ɗan shekara 10, Abdallah Lawali.

Bayanai sun ce ’yan uwan junan biyu sun aikata wannan ta’asa ce a ranar 7 ga watan Maris a unguwar Sarkin Yamma da ke Ƙaramar Hukumar Jada.

Majalisar Ribas ta soma shirye-shiryen tsige Gwamna Fubara Trump zai tuntuɓi Putin kan yaƙin Ukraine

Sanarwar da rundunar ’yan sandan ta fitar ta ce an kama ababen zargin ne da gangar jikin almajirin a cikin wani buhu, yayin da aka ƙwaƙulo kansa a cikin wani rami da suka binne a harabar gidansu.

Rundunar wadda ta ce yanzu haka bincike ya kankama a kan lamarin, ta kuma bayyana cewa ababen zargin sun yi iƙirarin aikata laifin da suka alaƙanta da sharrin shaiɗan.

Kwamishinan ’yan sandan jihar CP Dankombo Morris, ya tabbatar da cewa za a yi adalci a lamarin, yayin da yake kira ga al’umma da su kasance masu lura da miƙa rahoton duk wani motsi da su aminta da shi ba zuwa ofishin mahukunta mafi kusa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Adamawa Wa da ƙani

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama gungun masu fashi a kan hanyar Katsina zuwa Kano

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta kama gungun mutane 11 da ake zargi da kasancewa ’yan fashi da makami da ke addabar matafiya a kan hanyar Katsina zuwa Kano.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Abubakar Aliyu, ya shaida wa manema labarai a ranar Laraba a Katsina cewa waɗanda ake zargin sun kware wajen tare hanyoyin zuwa Sha’iskawa-Charanchi da Katsina-Kankia-Kano, suna kwace dukiyoyin matafiya.

DSS ta cafke tsoffin jami’anta 2 kan aikata zamba Kotu ta daure kocin kwallon kafa a Kano shekara 8 saboda aikata luwadi

Ya bayyana sunayen waɗanda aka kama da suka haɗa da Dikko Ma’aru, Dardau Kabir, Muntari Musa, Labaran Amadu, Usman Ma’aru, Lawal Zubairu, Nasiru Sanusi, da Adamu Kabir.

Sauran sun haɗa da Abdullahi Zubairu, Muhammad Usman da Sale Shehu, dukkaninsu ’yan tsakanin shekaru 21 zuwa 35.

Ya ce, “Nasarar ta samu ne a ranar Lahadi da misalin ƙarfe 10 na safe lokacin da aka cafke ɗaya daga cikin gungun yayin da yake ƙoƙarin sayar da wasu kayayyakin da suka yi fashin su, bayan samun sahihin bayanan sirri.

“Bayan samun wannan bayani, jami’anmu sun bi sahu suka kama wanda ake zargin, lamarin da ya kai ga kama sauran ’yan gungun,” in ji shi.

Kakakin ’yan sandan ya ce yayin bincike, an samu agogo guda 80, wayoyi 9 da wuka daga hannun waɗanda ake zargin a matsayin shaidu.

Ya ƙara da cewa Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Bello Shehu, ya yaba da ƙoƙarin jami’an da suka gudanar da aikin, tare da nuna godiya ga goyon bayan jama’a.

Aliyu ya rawaito Kwamishinan yana ƙara kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da muhimman bayanai da za su taimaka wajen yaƙi da laifuka a jihar.

Ya kuma ce za a gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ’yan sandan bogi 5 a Kano
  • Matasa sun yi zanga-zanga kan yunwa a Adamawa
  • Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn
  • Wani mutum ya ƙona tsohuwar budurwarsa a Oyo
  • An ceto mutane 3 da aka yi garkuwa da kama wasu a Bauchi
  • ’Yan sanda sun kama gungun masu fashi a kan hanyar Katsina zuwa Kano
  • DSS ta cafke tsoffin jami’anta 2 kan aikata zamba
  • An kama mutum shida yayin da ‘yan sanda suka kubutar da mutane uku da aka yi garkuwa da su a Bauchi.
  • Kotu ta daure kocin kwallon kafa a Kano shekara 8 saboda aikata luwadi