Ko Barcelona Ta Kama Hanyar Lashe Gasar Laliga Ta Bana?
Published: 17th, March 2025 GMT
A daren ranar Lahadi Barcelona ta buga wasa mafi kayatarwa a wannan kakar wasanni ta bana bayan ta doke abokiyar karawarta Athletico Madrid duk da cewar Athletico din ta jefa kwallaye biyu a ragar Barcelona a minti 70 na wasan.
A kokarin da take yi na sake darewa kan teburin Laliga, Barcelona ta zura kwallaye 4 a cikin minti 20 domin komawa gida da maki uku, Lewondowski, Ferran Torres da Lamine Yamal ne su ka jefawa Barcelona kwallayenta.
Julian Alvarez na Athletico Madrid ya fara bude kasuwa a Wanda Metropolitano tun kafin zuwa hutun rabin lokaci, Alexander Sorloth ne ya kara ta biyu a minti na 70 da fara wasa lokacin da Conor Gallagher ya bashi kwallo cikin yadi na 18.
Barcelona na matsayi na daya da maki 60, inda suke da maki daya da Real Madrid dake matsayi na biyu, amma kuma Barcelona na da wasa daya a hannu wanda basu buga ba sakamakon mutuwar babban likitan kungiyar, Atletico ta ci gaba da zama a matsayi na uku akan teburin gasar Laliga.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Barcelona
এছাড়াও পড়ুন:
Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran
Bayan harin da gwamnatin Sahayoniya ta kai kasarmu, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya aike da sako ga al’ummar Iran. Ga sakon kamar haka
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai
Al’ummar Iran masu daraja!
Gwamnatin yahudawan sahyoniya ta hanyar aikata wani laifi da sanyin safiyar yau, ta sake bayyana munanan dabi’arta da fasadi.
Ta hanyar kai hari dole ne wannan ya fuskanci hukunci mai tsanani.
A wannan harin makiya, kwamandoji da masana kimiyya da dama sun yi shahada.
Wadanda suka gaje su kuma da abokan aikinsu za su ci gaba da aiki nan take akan wannan tafarki, godiya ta tabbata ga Allah.
Ta hanyar wannan danyen aiki, gwamnatin Sahayoniya ta kaddara akan ta cewa zata fuskanci martini mai radadi.