Leadership News Hausa:
2025-11-19@16:28:22 GMT

Ko Barcelona Ta Kama Hanyar Lashe Gasar Laliga Ta Bana?

Published: 17th, March 2025 GMT

Ko Barcelona Ta Kama Hanyar Lashe Gasar Laliga Ta Bana?

A daren ranar Lahadi Barcelona ta buga wasa mafi kayatarwa a wannan kakar wasanni ta bana bayan ta doke abokiyar karawarta Athletico Madrid duk da cewar Athletico din ta jefa kwallaye biyu a ragar Barcelona a minti 70 na wasan.

A kokarin da take yi na sake darewa kan teburin Laliga, Barcelona ta zura kwallaye 4 a cikin minti 20 domin komawa gida da maki uku, Lewondowski, Ferran Torres da Lamine Yamal ne su ka jefawa Barcelona kwallayenta.

Yunkurin Neman ‘Yancin Kan Taiwan Ya Shaida Yunkurin Lai Ching-te Na Neman Mulki Irin Na Kama Karya Ta Hanyar Demokuradiyya Ba Don Tarbiyantar Da Mutane Nake Yin Fim Ba -Amina Shehu Lulu

Julian Alvarez na Athletico Madrid ya fara bude kasuwa a Wanda Metropolitano tun kafin zuwa hutun rabin lokaci, Alexander Sorloth ne ya kara ta biyu a minti na 70 da fara wasa lokacin da Conor Gallagher ya bashi kwallo cikin yadi na 18.

Barcelona na matsayi na daya da maki 60, inda suke da maki daya da Real Madrid dake matsayi na biyu, amma kuma Barcelona na da wasa daya a hannu wanda basu buga ba sakamakon mutuwar babban likitan kungiyar, Atletico ta ci gaba da zama a matsayi na uku akan teburin gasar Laliga.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Barcelona

এছাড়াও পড়ুন:

Masu ibadar Umara 42 sun mutu a hatsarin mota a hanyar zuwa Makka

Wasu masu ibadar Umara 42 sun mutu bayan da motarsu ta yi taho-mu-gama da wata tankar mai a kusa da birnin Madina da ke kasar Saudiyya.

Dukkan masu ibadar ’yan kasar Indiya ne, kuma hatsarin ya ritsa da su ne a kan hanyarsu ta zuwa Makka bayan kammala ziyara a birnin Madina.

Ministan harkokin wajen Indiya Dakta S. Jaishankar ya bayyana cewa mutum daya daga cikin fasinjojin ya tsallake rijiya da baya a hatsarin da ya auku da tsakar daren Litinin.

Hatsarin ya auku ne a bayan da motar safa mai daukar mutum 43 da masu ibadar suke ciki ta yi karo gaba-da-gaba da wata tankar mai.

’Yan ta’adda sun sace dalibai 25 a dakunan kwanansu a Kebbi NELFUND ya raba wa ɗalibai tallafin karatu na Naira Biliyan 116 

A sakon ta’azaiyyarsa ga iyalan mamatan, Ministan harkokin wajen Indiya, ya bayyaan cewa ofisoshin jakadancin kasar ke Saudiyya, na bayar da cikakken tallafi ga masu Umarar da hatsarin ya rusta da su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Saudiyya za ta kara hannun jarinta a Amurka zuwa dala tiriliyan daya
  • Barau FC ta doke Enugu Rangers a Firimiyar Najeriya
  • Mataimakin Shugaban Iran Na Daya Ya Gana Da Prime Ministan Rasha A Birnin Mosko
  • Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana
  • CAF ta fitar da ’yan wasa uku da suka rage a takarar gwarzon Afirka na bana
  • Gobara ta laƙume rayukan yara biyu ’yan gida ɗaya a Ribas
  • Masu ibadar Umara 42 sun mutu a hatsarin mota a hanyar zuwa Makka
  • Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka
  • Najeriya ba za ta buga kofin duniya ba karo na biyu a jere
  • Ɗan Najeriya ya kashe mahaifinsa, ya yanki ƙannensa da wuƙa a Amurka