Aminiya:
2025-07-06@16:30:37 GMT

Ambaliyar ruwa ta yi ajalin mutum 50 a Amurka

Published: 6th, July 2025 GMT

Hukumomi a Jihar Texas ta Amurka sun ce gomman mutane sun riga mu gidan gaskiya ciki har da kananan yara sakamakon wata mummunar ambaliyar ruwa a ranar Asabar.

Sai dai ya zuwa yau Lahadi, adadin wadanda suka mutu sun kai 50 ciki har da kananan yara 15 yayin da ake ci gaba da aikin ceto wadanda lamarin ya rutsa da su kamar yadda wani babban jami’in dan sanda na yankin, Larry Leitha ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na AFP.

An kama ɗan Najeriya yana taimaka wa Rasha a yaƙinta da Ukraine Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 41 a Nijar

Tuni dai Shugaba Donald Trump ya sanar da cewa gwamnati na yin duk mai yiwuwa wajen kai dauki yankin na Texas, inda ya ce shi da mai dakinsa Melania na mika sakon jaje da ta’aziyya ga iyalan wadanda suka mutu.

Trump ya kara da cewa jami’an hukumar kashe gobara da sauran jami’an agaji na ta fadi tashin kubutar da al’umma tare kuma da kokarin dakile tasirin ambaliyar.

Baturen ’yan sandan yankin Kerr County, ya sanar da cewa masu aikin ceto sun yi nasarar kubutar da mutane sama da 800 yayin da ake ci gaba laluben kananan yara galibinsu mata da aka nema aka rasa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa Jihar Texas kananan yara

এছাড়াও পড়ুন:

NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

Dantsoho wanda ya samu wakilicin Babban Manajan a Hukumar ta NPA Femi Oyewole, ya bayyana cewa, Shugaban Hukumar ta NPA, Hukumar ta mayar da hankali wajen ganin cewa, ana kare kimar Tekunan kasar.

“Hadurran zuba baraguzan kusan a kurkusa suke, wanda kuma, suke ci gaba da karuwa, wanda hakan ya nuna cewa, akwai matukar bukatar a dakile yadda ake duba baragunzan, a cikin Tekunan, baki daya,” Inji Dantsoho.

Ya ci gaba da cewa, Hukumar ta NPA bata yi kasa a guiwa ba, wajen daukar matakan da suka kamata, domin magance wannan matsalar.

“Duba da cewa, muna gudanar da ayyukan NPA yadda ya kamata da kuma bin ka;idojin da ke tafiyar da Hukumar, musamman wajen bai wa kayan Hukumar da ke a daukacin Tashoshin Jiragen Ruwan kasar kariya, kamar yadda suka kasance a matakin na kasa da kasa na dakile gurbatar da Jiragen Ruwa ke janyo wa, musamman duba da kundin tsari na (MARPOL 73/78), za mu ci gaba da lalubo da mafita kan zubar baraguzai a Tekunan kasar,” A cewarsa.

Shugaban ya kara da cewa, kayan aikin NPA na bukatar a samar masu kariyar da kamata, musamman ta hanyar bai wa Jiragen ruwa da ke tsayawa a Tashoshin kariyar da ta kamata.

Dantsoho ya bayyana cewa, NPA akai-akai ta kan tabbatar da ana ci gaba da tsaftace Tekunan daga kalubalen baraguzan da duk wata bola, da ake zubawa a cikin Tekunan kasar a daukacin Tashohin Jiragen Ruwan kasar.

Shugaban ya yi nuni da cewa, ta hanyar kwashe baraguzan da sauran bolar robobin da ake zubawar a cikin Tekunan ne, kadai, za a iya kare rayuwar dabbobin da ke rayuwa a cikin Tekunan tare da kuma samar wa Jiragen Ruwan saukin yin zirga-zirga a kan Tekunan kasar.

Shi kuwa a na sa jawabin a wajen taron Babab Sakataren Cibiyar kungiyar masu fito kaya a Jiragen Ruwa na kasa Dakta Pius Akutah, yabawa kungiyar ta wakilan masu wallafa rahotanin a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar kan zabo wannan maudu’in domin a tattauna a kansa

Ya kuma jaddda bukatar da a tabbatar da ana tsaftace hanyoyin Ruwa da ke a Tekunan kasar, musamman domin Jiragen Ruwan da ke hawansu, su samu saukin tafiya akai ba tare da wata tangarda ba.

Akutah, wanda Mataimakin Darakata a sashen sanya ido na cibiyar ya wakilce shi a wajen taron Adeshina Sarumi, ya yi nuni da cewa, samun baraguzan a hanyoyin Ruwan na haifar da cikas ga zirga-zirgar Jiragen Ruwan.

Shi kuwa Manajin Darakta na Hukumar NIWA Bolaji Oyebamiji, ya bukaci masu ruwa da tsaki a fannin da su yi dukkan mai yuwa, domin a dakile wannan kalubalen da ake fuskanta, musaman ta hanyar wyar da kan alummar da ke da zama a daura da Tekunan kasar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta Bukaci Gudanar da Bincike Kan Sacewar jami’ar Diblomasiyyar kasar A Lebanon Shekaru 43 Da Suka gabata
  • Akalla Mutane 52 Suka Rasa Rayukansu Saboda Ambaliyan Ruwan Sama A Jihar Texas Na Kasar Amurka
  • Lebanon: Mutum Daya Ya Yi Shahadi A Wani Hari Na HKI
  •  IRGC: Duk Wani Wuce Gona Da Iri Na ‘Yan Sahayoniya Zai Gaggauta Rushewarsu
  • Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu
  • NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya
  • NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku
  • Majalisar Jigawa Ta Isa Roni A Ci Gaba Da Rangadin Kananan Hukumomi
  • Ambaliya da iska sun rushe gidaje 171 a watanni biyu a Gombe – SEMA