Imam Khaminae Ya Halarci Makokin Ashoora A Gidansa A Tehran
Published: 6th, July 2025 GMT
Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya halarci zaman makokin da aka gudanar a hussainiyar Imam Khomaini (q) da cikin gidansa a nan birnin Tehran a daren Ashoorah a jiya Asabar da yamma.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Hujjatul Islam Masaoud Ali wanda ya karanta makokin yana fadar cewa, kasar Iran zata dauki darasi daga Imam Hussain (a) na rashin mika kai da azzalumai.
Ya kuma bayyana yunkurin da Iraniyawa suke yi a halin yansu yana daga cikin gwagwarmayan duniya don fuskantar azzaluman duniya karkashin jagorancin HKI da Amurka.
Ya kuma kara da cewa musulunci ne yake gaba da gaba da kafircin duniya a cikin yakin kwanaki 12 wanda HKI da Amurka suka jagoranta kan JMI. Kuma wannan yunkirin da sauran masu gwagwarmaya a duniya zasu ci gaba da gwagwarmaya tare da jagorancin Imam Sayyid Aliyul Khaminae. Wannan dai shi ne bayyanar Jagoran a karon farko bayan yakin kwanaki 12.
Malamin ya kara da cewa, iraniyawa ba zasu mika kai ba har zuwa nasara kamar yadda muka koya daga Imam Hussain (a) hakan a ranar Ashoorah.
A lokacinda Mahmoud Karimi zai karanta makokin an ga Imam Khaminae (H) yana fadawa Karimi wani abu a kunnensa , inda daga baya Karimin ya bayyana cewa ya umurce shi y ace, kasata zaki wanzu a zuciyata da raina.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
’Ya’yana na da ’yancin mallakar filaye a Abuja – Wike
Ministan Babban Birninn Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya musanta labarin cewa ya yanka wa ’ya’yansa manyan filaye a Abuja, inda ya ce in ma haka ne suna da hakki a matsayinsu na ’yan Najeriya.
Ana dai zargin Wike da ba biyu daga cikin ’ya’yansa fili mai fadin murabba’in hekta 2,082, dayan kuma mai fadin hekta 1,740, wanda aka kiyasta darajarsu ta haura Naira tiriliyan tara.
Da yake zantawa da ’yan jarida a Abuja ranar Alhamis, Wike ya karyata labarin na cewa ya ba ’ya’yan nasa filayen a unguwannin Maitama da Asokoro.
Makusantan Gwamnatin Buhari da suka shiga haɗakar ADC Filato: Mahara sun cire hannun matashi a kan hanyar komawa gida daga jana’izaTo sai dai duk da haka, ya kare batun, inda ya ce a matsayin su na ’yan Najeriya, su ma sun cancanci su mallaki filayen matukar dai an bi ka’ida.
“Alal misali, amma ba wai na amsa haka ba ne, a ce ’ya’yana sun nemi filayen, shin ba su cancanta a ba su ba ne? ko su ’yan Ghana ne? ko kuwa a’a, kawai saboda ni ina minista shi ke nan ba su cancanta ba?,” in ji Wike.
Ministan ya zargi wasu mutane da ya ce ba su da suna daga jihar Adamawa da kitsa zancen domin kawai su bata masa suna.
“Da farko ma ka fara lissafa hekta 2,000 na fili sai ka fada min a ina za ka sami hakan a Asokoro da Maitama. Na san daga jihar Adamawa aka shirya wannan kitimurmurar,” in ji shi.