Kamfanin jiragen sama na UAE airlines ko emirate ya sake farfado da zirga zirga zuwa kasar Iran bayan da aka rufe sararin samaniyar kasar Iran a ranar 13 ga watan Yunin da ya gabata.

Jaridar National ta kasar Amurka ta bayyana cewa kasashe da dama a duniya sun dakatar da zirga zirga zuwa JMI saboda yakin da HKI da Amurka suka kai mata daga 13 ga watan zuyi har zuwa kwanaki 12.

Labarin ya kara da cewa kasashen Iraki da Jordan sun dakatar da zuwa kasar Iran saboda yaki kuma saboda gwamnatin Iran ta hana jiragen sama tashi ko kuma zuwa kasar.

A ranar Alhamis ne JMI ta gabata ne hukumomin Iran suka bude sararin samaniyar kasar wanda ya nuna al-amura suna komawa kamar yadda suke bayan yakin kwanaki 12.  A halin yanzu dai tashar jiragen saman na Esfahan ne kawai ba’a sake budewa ba, mai yuwa sai kwani m asu zuwa idan an kammala gyare gyaren da yakamata a yi, bayan hare-haren da HKI ta kai mata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

2027: Ana raɗe-raɗin Sanata Lamiɗo zai fice daga APC zuwa ADC

Jita-jita ta fara ƙarfi cewar Sanata Ibrahim Lamiɗo da ke wakiltar Sakkwato ta Gabas a Majalisar Dattawa, na shirin ficewa jam’iyyar APC zuwa ADC.

Wannan jita-jita ta fara ƙarfi ne bayan da wasu ‘yan siyasa suka haɗu don kafa sabuwar jam’iyya mai suna ADC da nufin kayar da APC a zaɓen 2027.

Gonakin Koko: Mata sun yi barazanar zanga-zanga tsirara a Kuros Riba Kwankwaso ba zai yi mana takara a 2027 ba — NNPP

A cewar wasu, Sanata Lamiɗo ba ya mu’amala da gwamnatin APC a jihar inda alaƙarsa ta fi ƙarfi da ‘yan adawa.

Wannan ne ya sa ake ganin ba zai tsaya takara a APC ba a 2027.

Wani ɗan siyasa da ya nemi a sakaya sunansa ya ce Sanata Lamiɗo ba ya ga maciji da Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko da Gwamna Ahmad Aliyu.

A cewarsa, “Sama da shekara ɗaya ba mu ga Sanata Lamiɗo a taron gwamnati ko na APC ba. Don haka ba za mu yi mamakin ficewarsa ba.”

Wani magoyin bayan APC, Kabiru Wurno, ya ce yana da tabbacin cewa Sanatan zai koma ADC.

“Lamiɗo yana son sake tsayawa takara a 2027, amma da wuya APC ta ba shi dama saboda ba ya tare da manyan jagororinta. Dole ya nemi wata hanya.”

Shu’aibu Muhammad daga Sabon Birni, ya bayyana rashin jin daɗinsa kan yiwuwar ficewar Sanatan.

“Da zai shirya da Wamakko, da za su yi ƙarfi tare. Siyasar Gabas tana buƙatar haɗin kai.”

Shi kuwa Ya’u Muhammad daga Goronyo ya ce, “Idan har Sanata Lamiɗo zai fice daga APC, muna tare da shi. Shi mutum ne da ke tallafa wa matasa da marasa galihu.”

Wani makusancin Sanatan ya ce ba zai ce uffan kan lamarin ba, zai bar Sanatan ya yi ƙarin haske.

Sai dai duk da ƙoƙarin jin ta bakin Sanata Lamiɗo haƙar Aminiya ba ta cimma ruwa ba.

Yanzu dai jama’a da dama na dakon jiran hukuncin da Sanatan zai ɗauka kafin babban taron jam’iyyar ADC da ke tafe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Akalla Mutane 52 Suka Rasa Rayukansu Saboda Ambaliyan Ruwan Sama A Jihar Texas Na Kasar Amurka
  • 2027: Ana raɗe-raɗin Sanata Lamiɗo zai fice daga APC zuwa ADC
  • Ma’aikatan MDD Masu Kula Da Ayyukan Makamashin Nukliya Na Kasar Iran Su Fice daga Kasar
  • Shugaban Amurka Yace Yana Jiran Amsar Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60
  • Shugaban Kasar Iran Ya Rattaba Hannu Kan Daftarin Dakatar Da
  • Shugaban Amurka Yace Yana Jirin Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60
  • An Bude Mafiya Yawan Tashoshin Jiragen Sama A Iran Bayan Tsaida Yaki
  • NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku
  • Kwamandan Sojojin Iran Ya Ziyarci Gidan Babban Jami’in Sojin Kasar Da Ya Yii Shahada Lokacin Yakin Baya-Bayan Nan