Ba A Taɓa Shugaban Ƙasar Da Ya Kai Mahaifina A Nijeriya Ba – Ɗan Shugaban Tinubu
Published: 17th, March 2025 GMT
Seyi Tinubu, ɗan shugaban kasa Bola Tinubu, ya bayyana cewa mahaifinsa shi ne shugaban Nijeriya mafi girma a tarihi, yana yaba wa shugabancinsa da himmarsa wajen bunkasa rayuwar matasa. A cikin wani faifan bidiyo da ya bayyana ranar Litinin, Seyi ya furta wannan magana yayin da yake jawabi ga taron matasa a jihar Adamawa.
Ya ce, “Shi ne shugaban Nijeriya mafi girma a tarihi,” yana mai cewa mahaifinsa ya ba da fifiko ga ci gaban tattalin arziki da samar da dama ga matasa.
Ya kara da cewa, “Shi ne kawai shugaban da ya kiyaye mutanenku a gida, tun lokacin da ya kasance gwamna har ya zama shugaban kasa. Shugaban da ya dauki matasa da muhimmanci, ya samar da dandali don matasa su zama wasu.” Seyi ya kuma bayyana cewa gwamnatin mahaifinsa tana kan kirkiro tattalin arzikin da zai amfanar da kowa, yana mai cewa, “Shi ne kawai shugaban da ba shi da nufin wadatar da kansa.”
Dalilin Da Ya Sa Tinubu Ya Nada Jega A Matsayin Mai Ba Shi Shawara Kan Samar Da Sauyin Noma Da Kiwo Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Karramawar Da Sojoji Suka Yi Wa Seyi TinubuKwanan nan, Seyi Tinubu ya shiga cikin ayyukan al’umma, musamman a jihohin arewacin Najeriya, inda aka gan shi yana rarraba kayayyakin abinci. A watan Maris, ya halarci wurare a jihar Kano, inda ya gana da mutane da dama ciki har da shugaban jam’iyyar NNPP na jihar, Hashimu Dugurawa, wajen buda bakin azumin Ramadan.
Haka kuma, Seyi ya ziyarci jihar Yobe a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarinsa na shiga cikin al’umma da matasan Nijeriya. Ayyukansa na ziyartar jihohi da bayar da tallafi ga al’umma sun nuna kokarin da yake yi na kara kusantar jama’a da kuma tallafawa manufofin mahaifinsa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
Hukumar Fensho ta Jihar Jigawa da Kananan Hukumomin jihar ta shirya fara aikin tantance ‘yan fansho da ke cikin tsarin.
Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, Alhaji Muhammad K. Dagaceri ne ya bayyana haka yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Gidan Fansho, inda shugabannin kungiyar ‘Yan Fansho ta Najeriya reshen Jigawa suka halarta.
A cewarsa, an shirya fara aikin tantancewar ne daga ranar Litinin, 5 ga Mayu, 2025.
Alhaji Dagaceri ya bayyana cewa, an shirya hakan ne da nufin sabunta tsarin biyan fansho tare da tabbatar da ingancin bayanai.
Ya ce, aikin tantancewar zai gyara wasu ‘yan kura-kurai da suka kunno kai a cikin shekaru uku da suka gabata, da kuma tabbatar da ingantattun bayanai a jadawalin biyan fansho.
Ya kara da cewa, wannan yunkuri ya yi daidai da kudirin jihar gwamnati na tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkokin mulki, tare da bai wa ‘yan fansho dama su gyara duk wani bayanin da bai cika ba a takardunsu.
Shi ma da ya ke jawabi, Akanta Janar na Jihar, Alhaji Abdullahi S.G. Shehu, ya jaddada cewa aikin tantancewar zai bai wa ‘yan fansho damar sabunta bayanansu da suka bace ko suka canza a takardunsu.
Saboda haka, ya bukaci dukkan ‘yan fansho daga ma’aikatun gwamnati, sassan hukumomi, kananan hukumomi da kuma hukumomin ilimi na kananan hukumomi da su halarci tantancewar a ranar da aka tsara kamar yadda yake cikin jadawalin aikin.
A jawabinsa, Shugaban kungiyar kananan hukumomi ALGON ta Jihar Jigawa, Farfesa Salim Abdurrahman, ya tabbatar da cikakken goyon baya daga shugabannin kananan hukumomi 27 domin cimma burin aikin.
Shugaban na ALGON wanda shugaban karamar hukumar Malam Madori, Alhaji Salisu Sani ya wakilta, ya bukaci ‘yan fanshon da su ba da cikakken haɗin kai don samun nasarar shirin.
Shi ma Shugaban hukumar, Dr. Bilyaminu Shitu Aminu, ya bukaci ‘yan fansho daga sassa daban-daban da su ba da hadin kai domin cimma burin da aka sanya, tare da jaddada cewa su ziyarci sakatariyar kananan hukumominsu domin a tantance su.
Shugaban Kungiyar ‘Yan Fansho ta Najeriya reshen Jihar Jigawa, Alhaji Umar Sani Babura, ya yi alkawarin cewa kungiyar za ta bada cikakken goyon baya domin nasarar wannan shiri.
Dukkan ‘yan fansho daga Ma’aikatun Gwamnati, Kananan Hukumomi, da Hukumomin Ilimi na Kananan Hukumomi da ke cikin tsarin fanshon, ya zama wajibi su halarci wannan tantancewa a ranakun da aka tsara a jadawalin aikin.
Usman Muhammad Zaria