Seyi Tinubu, ɗan shugaban kasa Bola Tinubu, ya bayyana cewa mahaifinsa shi ne shugaban Nijeriya mafi girma a tarihi, yana yaba wa shugabancinsa da himmarsa wajen bunkasa rayuwar matasa. A cikin wani faifan bidiyo da ya bayyana ranar Litinin, Seyi ya furta wannan magana yayin da yake jawabi ga taron matasa a jihar Adamawa.

Ya ce, “Shi ne shugaban Nijeriya mafi girma a tarihi,” yana mai cewa mahaifinsa ya ba da fifiko ga ci gaban tattalin arziki da samar da dama ga matasa.

Ya kara da cewa, “Shi ne kawai shugaban da ya kiyaye mutanenku a gida, tun lokacin da ya kasance gwamna har ya zama shugaban kasa. Shugaban da ya dauki matasa da muhimmanci, ya samar da dandali don matasa su zama wasu.” Seyi ya kuma bayyana cewa gwamnatin mahaifinsa tana kan kirkiro tattalin arzikin da zai amfanar da kowa, yana mai cewa, “Shi ne kawai shugaban da ba shi da nufin wadatar da kansa.”

Dalilin Da Ya Sa Tinubu Ya Nada Jega A Matsayin Mai Ba Shi Shawara Kan Samar Da Sauyin Noma Da Kiwo Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Karramawar Da Sojoji Suka Yi Wa Seyi Tinubu

Kwanan nan, Seyi Tinubu ya shiga cikin ayyukan al’umma, musamman a jihohin arewacin Najeriya, inda aka gan shi yana rarraba kayayyakin abinci. A watan Maris, ya halarci wurare a jihar Kano, inda ya gana da mutane da dama ciki har da shugaban jam’iyyar NNPP na jihar, Hashimu Dugurawa, wajen buda bakin azumin Ramadan.

Haka kuma, Seyi ya ziyarci jihar Yobe a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarinsa na shiga cikin al’umma da matasan Nijeriya. Ayyukansa na ziyartar jihohi da bayar da tallafi ga al’umma sun nuna kokarin da yake yi na kara kusantar jama’a da kuma tallafawa manufofin mahaifinsa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka Ta Bar Baya Da KuraAfuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka Ta Bar Baya Da Kura

Kamar yadda rahotanni suka tabbatar, Shugaba Tinubu ya yi wa akasarinsu sassauci ne, bisa rahotannin da ke cewa; wadanda aka yanke wa hukuncin, sun nuna matukar nadama da kuma halin kirki. Haka zalika, ya yafe wa wasu saboda tsufa da samun sabbin fasahohin sana’o’i, ko shiga Jami’ar NOUN. Shugaba Tinubu ya kuma gyara rashin adalcin tarihi, wanda Turawan mulkin mallaka na Burtaniya suka yi wa Sir Herbert Macaulay, daya daga cikin masu kishin kasa a Nijeriya.

 

A takaice dai, kwamitin bai wa shugaban kasa shawara, kan jinkai, karkashin jagorancin babban mai shari’a; kuma ministan shari’a, Prince Lateef Olasunkanmi Fagbemi, ya bayar da shawarar yin afuwa ga fursunoni biyu da 15 da aka yankewa hukunci, wadanda 11 daga cikinsu sun rasu. Kazalika, kwamitin ya ba da shawarar yin afuwa ga fursunoni 82 tare da sassauta hukuncin dauri na fursunoni 65. Fursunonin bakwai da aka yanke wa hukuncin kisa, su ma sun shiga cikin jeren afuwar da shugaban kasar ya yi. Sannan, kwamitin ya ba da shawarar cewa; shugaban kasa ya mayar da hukuncin kisa zuwa daurin rai da rai.

 

Fagbemi ya gabatar da rahoton kwamitin a taron majalisar kasa, wanda shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta.

 

A bangare guda kuma, ‘yan Nijeriya da dama na fadin albarkacin bakinsu, dangane da wannan afuwa da shugaban kasa ya yi wa masu laifukan daban-daban, wasu na da ra’ayin cewa; mafi yawan wadanda aka yi wa afuwar, ‘yan kwaya ne da rikakkun ‘yan ta’adda da kuma wadanda tuni suka mutu. A cikin masu nuna takaicin nasu; akwai tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ‘yan siyasa, masu sharhi kan al’amuran yau da kullum, jam’iyyun adawa da kuma iyalai da sauran abokanan arziki da al’amarin ya shafa.

 

Iyalan marigayi Bilyaminu Ahmed Bello, na daya daga cikin wadanda suka bayyana rashin jin dadinsu, kan afuwar da shugaban kasa ya yi wa Maryam Sanda, wadda aka yankewa hukuncin kisa bisa laifin kashe mijinta, wadanda suka bayyana yin afuwar a matsayin wani mummunan zalinci da aka tafka musu.

 

A wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin da ta gabata dauke da sa hannun Dakta Bello Haliru Mohammed (Dangaladiman Gwandu), a madadin ‘yan’uwa, ‘yan’uwan marigayin sun bayyana matakin da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya dauka na yi wa Sanda afuwa a matsayin wani mummunan sake fama musu raunukan da suka samu da kuma rashin adalci ga dan’uwan nasu.

 

Iyalan Bilyaminun sun bayyana cewa, sun ji matukar takaicin sakin Maryam da aka yi, inda suka bayyana hakan; a matsayin wani yunkuri na dadada wa danginta tare da yin watsi da bacin ran da ya addabi ‘yan’uwa da sauran abokan arzikin marigayin.

 

Maryam, mai shekaru 37, na daya daga cikin mutum 175 da aka yanke wa hukunci, aka kuma yi wa afuwa da jin kai a ranar Alhamis da ta gabata, a karkashin ikon shugaban kasa.

 

A bangare guda kuma, kwatsam! Sai ga sanarwar mahaifin mijin Maryam Sandan cewa; shi da kansa ne ya roki Shugaban Kasa Tinubu, ya yi wa sirikar tasa afuwa.

 

A cewarsa, ya dade yana neman rokon a yi wa Maryam sassauci tare da afuwa, wacce ke fuskantar hukuncin kisa, tun bayan yanke mata hukuncin da aka yi.

 

Alhaji Ahmed Bello Isa, wanda ya bayyana hakan a wata tattaunawa ta hadin gwiwa da aka yi da shi a ranar Talatar da ta gabata a Abuja tare da Alhaji Garba Sanda, mahaifin Maryam, ya bayyana cewa; dalilinsa na yin hakan, saboda tausayi tare kuma son ganin an sako masa surukarsa, domin ta samu ta kula da ‘ya’yanta guda biyu, domin kuwa, kashe ta ba zai taba dawo masa da dansa ba.

 

Ya kara da cewa, “Na yafe wa Maryam da aka samu da laifin kisan dana, kafin a kammala shari’a, na yi iya kokarina na sanar da ‘yansanda da kotu cewa; ba na so a gurfanar da ita a gaban kuliya, domin kuwa jikoki kamar yadda suka rasa mahaifinsu, haka nan kuma za su rasa mahaifiya.

 

“Na dauki wannan a matsayin iftila’i, wanda Allah ya jarrabe ni da shi, a kan abin da ya faru da dana, sannan kuma ko kadan ban ga laifin Maryam ba, amma a lokacin da aka yanke mata hukuncin kisa, addu’a na yi mata tare da rokon Allah ya ji kan ta da rahama, sannan na ce; idan aka kashe ta, wa zai kula da ‘ya’yanta guda biyu? Kawai za su girma ne a matsayin marayu, babu soyayyar uba, babu ta uwa,” in ji shi.

 

Da aka tambaye shi game da maganar da ‘yan’uwa suka yi na nuna damuwarsu kan afuwar da shugaban kasa ya yi mata sai ya ce; “Kowa yana da ‘yancin fadin albarkacin bakinsa a cikin iyalansa, amma a matsayina na mahaifinsa, na yafe mata.

 

Shi ma da yake yin nasa jawabin, Alhaji Garba Sanda, mahaifin Maryam, ya nuna matukar godiyarsa ga Alhaji Bello da sauran daukacin iyalansa, bisa irin halin da suka tsinci kansu a ciki; wanda ba kasafai suke nunawa ba.

 

Iyalan biyu, sun bayyana cewa, sun zabi afuwa, tausayi da kuma imani fiye da ciwon da yake damun su, sannan kuma sun himmatu wajen hada kai; domin renon yaran biyu, cikin kwanciyar hankali da soyayya.

 

Shi ma a nasa bangaren, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, ya zargi Shugaban Kasa Bola Tinubu, da yin amfani da ikon shugaban kasa na jin kai, ta hanyar yin afuwa ga mutum 175, yana mai cewa; matakin “ya gurgunta adalci”, sannan kuma yana da matukar hadari ga rashin bin doka da oda.

 

A cikin wata sanarwa da Atikun ya fitar, ta shafinsa na D a ranar Lahadin da ta gabata ya ce; hakkin yin afuwa, ba yana nufin rashin yin adalci ba ne ko tauye wa wani hakkinsa ba.

 

Har ila yau, Atiku ya soki shigar da mutanen da aka samu da aikata manyan laifuka, yana mai cewa; sakamakon wadanda aka yi wa afuwar, hakan na iya raunana imanin wasu daga cikin mutane tare da karfafawa wasu gwiwa, wajen ci gaba da aikata muggan laifuka.

 

Ya kara da cewa, bai kamata a bar yin afuwa ko jin kai ya hada su jera da aikata muggan laifuka da kuma rage aiwatar da adalci ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa October 16, 2025 Manyan Labarai Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC October 16, 2025 Manyan Labarai Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC October 16, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
  • Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya
  • ‘Yan Nijeriya Na Dab Da Fita Daga Halin Kuncin Talauci – Shettima 
  • Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Kura
  • Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka Ta Bar Baya Da KuraAfuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka Ta Bar Baya Da Kura
  • Shugaban Kasar Sudan Yana Ziyarar Aiki A Kasar Masar
  • Jihar Kwara Zata Haɗin Kai Da Masu Ruwa Da Tsaki Wajen Horas Da Matasa Fasahar AI
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sanata Ahmed Wadada Aliyu Murnar Ranar Haihuwa
  • Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Super Eagles Murnar Samun Cancantar Shiga Gasar Kwallon Kafa Ta Duniya