Yemen: Amurka Ta Sake Kai Wani Harin A Kasar Yemen
Published: 17th, March 2025 GMT
Kasar Yemen ta sanar da cewa Amurka da ta sake kai wasu hare-haren a gundumar Hudaidah akan wani kamfani na auduga.
Kamfanin dillancin labarun “Mehr” na Iran ya nakalto majiyar Ansarullah ta kasar Yemen din tana cewa; Sojojin na Yemen sun kai hare-hare da makamai masu linzami har 18 akan jiragen ruwa na dakon jiragen yaki “USS Troman” hari.
Kakakin sojan kasar Yemen ne janar Yahya Sari ya sanar da kai hare-hare na martani akan jiragen yakin Amurka.
Tun daga ranar Asabar din da ta gabata ne dai jiragen yakin Amurka da na Birtaniya su ka rika kai wa Yemen hare-hare da sun yi sanadiyyar shahadar mutane da dama.
Yankunan da harin ya shafa sun hada biranen San’aa da kuma Sa’adah, sai kuma Hudaidai.
A gefe daya shugaban kungiyar Ansarullah ta Yemen Sayyid Abdulmalik Husi, ya ce: hare-haren ta’adanci wadanda sojojin Amurka da Burtaniya suka kai kan yankuna da dama a kasar ba za su hana mutanen kasar ci gaba da kare Falasdinawa a Gaza ba.
Haka nan kuma ya kara da cewa: Za su ci gaba da kai hare hare a kan jiragen HKI da na Burtaniya da na Amurkan, masu wucewa ta tekun malia kamar yadda ta bayyana tun farko.
Kungiyar Ansarullah ta kasar yemen dai ta tallafawa Falasdinawa a yakin tufanul Aksa wanda aka fara a ranar 7 ga watan octoban shekara ta 2023, har zuwa lokacin da aka tsagaita wuta tsakanin Falasdinawa a Gaza da HKI a ranar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025.
Mayakan “Jubhatun-Nusrah’ Na Kasar Syria Sun Kai Hari Akan Iyakar Kasar Leabnon
A jiya Lahadi ne dai kungiyar ta ‘yan ta’adda ta kai hare-hare akan iyakar Lebanon ta yankin Hermul
Ma’aikatar tsaron Syria ta fitar da wata sanarwa da a ciki ta riya cewa; harin nata martani akan wani hari da aka kai a can cikin kasar wanda ta jinginawa HIzbullah, da kuma ya yi sanadiyyar mutumar jami’an tsaro uku.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kai hare hare Kasar Yemen kasar Yemen
এছাড়াও পড়ুন:
Majid Majidi Na Iran Ya Sami Kyauyar Girmamawa Daga Cibiyar Fina-finai Na “Eurasia Dake Kasar Rasha
Fitacce mai shirya fina-finai dan kasar Iran Majid Majidi ya sami kyauta ta musamman a wurin bikin fina-finai na Eurasia, saboda gagarumar rawar da yake takawa a fagen shiryafina-finai da su ka shahada a duniya.
A ranar Alhamis din da ta gabata ne aka bude bikin a birnin Moscow wanda ya sami halartar ministan al’adu na kasar Rasha, Olga Lyubimova, mataimakin shugaban kasar Rasha, Vladmir Medinsky sai kuma jakadan jamhuriyar musulunci ta Iran a Rasha Kazem Jalali.
Shugaban Tsangayar FIna-finai ta Eurasia, Nikita Mikhalov ya jinjina wa Majid Majidi saboda fina-finan da ya yi da hakan ya sa aka ba shi kyauta ta musamma da ita ce lambar yabo ta “ Dimond Butterfly”.
A jawabin da ya gabatar, Majid Majidi ya bayyana cewa; Mafi yawancin fina-finan da yake yi, suna da alaka ne da kananan yara da kuma matasa. Haka nan kuma ya ambaci da yin ishara da kananan yaran Gaza wadanda ake zalunta, yana mai fatan ganin zaman lafiya mai dorewa ya mamaye duniya.
Gabanin mika masa lambar yabon, an nuna wasu daga fina-finan da Majidi ya shirya da su ka hada da fim din tarihin manzon Allah ( s.a.w) mai taken; Muhammad; Manzon Allah.
Kimar lambar yabon da aka bai wa Majid Majidi dai ta kai dalar Amurka miliyan daya, da wani dan kasar China mai shirya fina-finai Xh Zheng ya samu,saboda fim dinsa mai taken: “Against the Current”.
Shi dai Majid Majidi an haife shi ne a Tehran a 1959, yana kuma daya daga cikin fitattun masu shirye-finai a Iran.
A shekarar 1997 fim dinsa mai taken; The children of Heaven,’ ya shiga takarar samun kyautar fina-finai ta Amurka.
Wasu fina-finansa da su ka yi suna a duniya sun hada; The Color of Paradise (1999), sai Baran (2001).
Fina-finansa dai sun fi mayar da hankali ne akan matsaloli na kananan yara, talaucii, jajurcewa a gwagwarmaya da hakan ya sa shi yin fice a cikin gida da kuma a duniya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Benin : Har yanzu Shugaba Patrice Talon ne a kan mulkin_fadar shugaban kasa December 7, 2025 Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi) December 7, 2025 Hamas : ‘’Babu batun kwance damarar makamai matuƙar Isra’ila ta ci gaba da mamaya’’ December 7, 2025 Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila December 7, 2025 Masar : ba za mu bari a yi amfani da iyakar Rafah ba don korar Falasdinawa December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168 December 7, 2025 Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167 December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166 December 7, 2025 Rwanda Da Amurka Sun Rattaba Hannu Kan Tallafin Dalar Amurka Miliyon $228 Na Kiwon Lafiya December 7, 2025 Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba December 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci