HausaTv:
2025-12-14@16:02:37 GMT

Yemen: Amurka Ta Sake Kai Wani Harin A Kasar Yemen

Published: 17th, March 2025 GMT

Kasar Yemen ta sanar da cewa Amurka da ta sake kai wasu hare-haren a gundumar Hudaidah akan wani kamfani na auduga.

Kamfanin dillancin labarun “Mehr” na Iran ya nakalto majiyar Ansarullah ta  kasar Yemen din tana cewa; Sojojin na Yemen sun kai hare-hare da makamai masu linzami har 18 akan jiragen ruwa na dakon jiragen yaki “USS Troman” hari.

Kakakin sojan kasar Yemen ne janar Yahya Sari ya sanar da kai hare-hare na martani akan jiragen yakin Amurka.

Tun daga ranar Asabar din da ta gabata ne dai jiragen yakin Amurka da na Birtaniya su ka rika kai wa Yemen hare-hare da sun yi sanadiyyar shahadar mutane da dama.

Yankunan da harin ya shafa sun hada biranen San’aa da kuma Sa’adah, sai kuma Hudaidai.

A gefe daya shugaban kungiyar Ansarullah ta Yemen Sayyid Abdulmalik Husi, ya ce: hare-haren ta’adanci wadanda sojojin Amurka da Burtaniya suka kai kan yankuna da dama a kasar ba za su hana mutanen kasar ci gaba da kare Falasdinawa a Gaza ba.

Haka nan kuma ya kara da cewa:  Za  su ci gaba da kai hare hare a kan jiragen HKI da na Burtaniya da na Amurkan, masu wucewa ta tekun malia kamar yadda ta bayyana tun farko.

Kungiyar Ansarullah ta kasar yemen dai ta tallafawa Falasdinawa a yakin tufanul Aksa wanda aka fara a ranar 7 ga watan octoban shekara ta 2023, har zuwa lokacin da aka tsagaita wuta tsakanin Falasdinawa a Gaza da HKI a ranar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025.

Mayakan “Jubhatun-Nusrah’ Na Kasar Syria Sun Kai Hari Akan Iyakar Kasar Leabnon

A jiya Lahadi ne dai kungiyar ta ‘yan ta’adda ta kai hare-hare akan iyakar Lebanon  ta yankin Hermul

Ma’aikatar tsaron Syria ta fitar da wata sanarwa da a ciki ta riya cewa; harin nata martani akan wani hari da aka kai a can cikin kasar wanda ta jinginawa HIzbullah, da kuma ya yi sanadiyyar mutumar jami’an tsaro uku.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kai hare hare Kasar Yemen kasar Yemen

এছাড়াও পড়ুন:

Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya

Ɗan wasan gaban Ƙungiyyar Ƙwallon Ƙafa ta Galatasaray ɗan asalin Najeriya, Victor Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasa na bana, a bikin bayar da kyaututtuka ta GQ Türkiye na maza na 2025.

Ɗan wasan mai shekara 26 ya sami kyautar mafi girma a bikin da aka gudanar mai ban sha’awa.

Matatar man Dangote ta rage farashin fetur zuwa N699 Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai

Ya sami kyautar ne saboda rawar da ya taka a Galatasaray a kakar wasa ta bara, inda ya zura ƙwallaye 37 kuma ya taimaka wajen zura ƙwallo sau bakwai a wasanni 41, wanda hakan ya sa Galatasaray ta lashe gasar Turkiya.

Osimhen ya karya tarihin Galatasaray na zama ɗan wasan da ya fi tsada a tarihin Ƙungiyar bayan ya koma akan kuɗi Yuro miliyan 75 daga Napoli.

Osimhen ya ci gaba da yin abin a yaba a wannan kakar, inda ya riga ya zura ƙwallaye 11 a wasanni 14 da ya bugawa ƙungiyar da ke birnin Istanbul.

Galatasaray na matsayi na ɗaya akan teburin babbar gasar ƙwallon ƙafa ta ƙasar Turkiyya da maki 36 a wasanni 15 da ta buga yayin da Trabzonspor ke matsayi na biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe mutum 11 da jikkata wasu 29 a bikin Yahudawa a Ostireliya 
  • Dan bindiga ya kashe sojojin Amurka biyu da wani farar hula a Siriya
  • DRC: Kungiyar M23 Ta Kwace Iko Da Wani Gari Mai Muhimmanci
  • Haɗin Kan Musulmai Da Kirista A Nijeriya Zai Kawo Saukin Matsalar Tsaro — Shehu Sani
  • Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman
  • Dantsoho Ya Yaba Wa Ƙoƙarin Oyetola Na Dawo Da Nijeriya Tsarin Sufurin Jiragen Ruwa Na Duniya
  • Sojoji sun daƙile harin ’yan ta’adda a Borno
  • Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare
  • Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara