“Za a lika sunayen tare da albashin ma’aikata a wurare masu mahimmanci a cikin harabar ma’aikatu, ofisoshin gwamnati da sakatariyar kananan hukumomi 44 na jihar don sauƙaƙe aikin,” in ji Faruk.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.

Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano

Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, ta tabbatar da rasuwar wasu mutum biyar sakamakon haɗura uku da suka auku a jihar.

Kakakin hukumar, Saminu Yusif Abdullahi, ya ce hatsrin farko ya faru ne da safiyar ranar Alhamis a unguwar Badawa Layin Day by Day ca Ƙaramar Hukumar Nassarawa.

Sojoji sun yi yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin Jirgin sojin sama ya yi hatsari a Neja

Lamarin ya faru ne a wani gida mai faɗin kafa 25 da 20 wanda ya kama da wuta.

Ma’aikatan kashe gobara sun ceto wata yarinya mai shekara 10 daga a cikin gidan, amma daga baya ta rasu a asibiti.

An bai wa iyayenta gawarta.

Hatsari na biyu ya faru ne a Ƙauyen Badume Kanawa da ke Karamar Hukumar Bichi.

Wani mutum mai shekara 65, Sa’idu Gada, yana aiki a cikin rijiya lokacin da igiyar da ta ke riƙe da shi ta tsinke, ya faɗa ciki.

Ɗansa mai shekara 20, Sani Isyaku, ya shiga rijiya domin ceto shi, shi ma ya maƙale.

Wani mutum na uku, Yakubu Abdullahi mai shekara 60, ya shiga domin taimakonsu, shi ma daga bisani ya faɗa cikin rijiyar.

Ma’aikatan hukumar sun fito da su daga rijiyar, amma sun riga sun rasu.

An miƙa wa ’yan sandan Badume gawarwakinsu.

A wani lamari na daban kuma, wani yaro mai shekara 10, Hassan Iliyasu Haruna, ya zame tare da faɗa wa rijiya a Ƙaramar Hukumar Danbatta.

Ma’aikatan hukumar kashe gobara sun ceto shi, amma daga baya ya rasu.

An miƙa wa mahaifinsa gawar yaron.

Daraktan Hukumar Kashe Gobara ta Kano, Sani Anas, ya ja hankalin jama’a da su daina shiga rijiya domin ceto mutane, domin a cewarsa hakan na da hatsari.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano
  • Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba
  • Dalilin da ya sa ’yan sanda suka kama ni — Muhuyi
  • Mutum 3 sun mutum yayin haƙar rijiya a Kano
  • Shugaban Majalisar Dattawan Akpabio ya Nemi Sanata Natasha ta Biya Shi Diyyar Biliyan 200
  • Amurka ta Faɗaɗa Jerin ƙasashen Afrika Da ta Sanya wa Takunkumin Visa
  • Jigajigan Majalisar Ribas 17 Sun Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
  • Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda
  • ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano
  • Gwamnatin Gombe da UNICEF sun tallafa wa yara masu fama ƙarancin abinci mai gina jiki