Aminiya:
2025-05-18@17:26:53 GMT

An kashe mafarauta 10 a Adamawa

Published: 29th, April 2025 GMT

Aƙalla wasu mutum 10 mafarauta sun rasa rayukansu yayin aikin ceto a ƙauyen Kopire da ke Ƙaramar Hukumar Hong ta Jihar Adamawa.

Shugaban ƙungiyar mafarautan Nijeriya reshen Arewa maso Gabas, Shawulu Yohanna ne ya tabbatar wa Aminiya hakan a ranar Talata.

Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal

A cewarsa, ajali ya katse hanzarin mafarautan ne yayin wani arbatu da mayaƙan Boko Haram da suka yi musu kwanton ɓauna a jeji.

Ya bayyana cewa, mafarautan sun tunkari maharan ne bayan samun bayanan sirri da ke nuna cewa suna shirin kai hari.

“Abin takaicin shi yadda ake yi wa Gwamnan Borno ƙafar ungulu a ƙoƙarin da yake yi na ganin an kawo ƙarshen wannan hare-hare a yankin,” in ji shi.

Yohanna ya bayyana damuwa kan yadda mayaƙan Boko Haram ke ci gaba da ƙara ƙarfi a bayan nan da ke zama abin fargaba ga mazauna yankunan da abin ya shafa.

“Mun samu labarin cewa wani jirgi mai saukar ungulu ne yake jigilar mayaƙan daga sansaninsu zuwa wuraren da suke sheƙe ayarsu ba tare fuskantar wata tirjiya ba.

“Amma ina mai tabbatar da cewa muddin Gwamnatin Tarayya ta ɗauki mataki ta hanyar tanadar makamai na zamani, za a kawo ƙarshen waɗannan maƙiya cikin lokacin ƙanƙani.”

Ya roƙi Gwamnatin Tarayya da ta tanadar wa mafarauta da ’yan sa-kai manyan makamai na zamani domin kawo ƙarshen mayaƙan Boko Haram a yankin.

Wannan harin dai na zuwa ne ƙasa da sa’o’i 12 da wasu ’yan ta’adda suka kashe fiye da mutum 30 ciki har da mata da ƙananan yara a ƙananan hukumomin Kala Balge da Gambarou Ngala da ke jihar.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Jihar Adamawa mafarauta

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 5 sun jikkata yayin da gidan mai ya ƙone ƙurmus a Ribas

Aƙalla mutum biyar ne sun jikkata bayan da gobara ta tashi a gidan man Nobpet da ke kusa da mahaɗar Sojojin Sama a garin Fatakwal, Jihar Ribas.

Gobarar ta kuma ƙone sama da motoci takwas da aka ajiye kusa da ofishin Hukumar Sufuri ta Jihar Ebonyi.

Sojoji sun kashe ’yan bindiga da ƙwato shanun sata 1000 a Taraba  Tinubu ya ƙaddamar da jirage 2, ya buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro

Ma’aikatan kashe gobara na Jihar Ribas tare da haɗin gwiwar na Sojojin Sama ne suka yi aiki tare har suka iya kashe gobarar.

Ɗaya daga cikin waɗanda abin ya shafa, Emmanuel Ninyaegwu, wanda direba motar haya ne, ya ce motarsa mai ɗaukar fasinja 18 ta ƙone gaba ɗaya.

Ya kuma ce shi da matarsa mai ɗauke da juna biyu sun kuɓuta da ƙyar daga gobarar.

“Na shirya domin ɗaukar fasinjoji zuwa Jihar Ebonyi. Ina buɗe but ɗin motata sai na ji ƙarar gobara.

“Nan take na kwanta a ƙasa, na tashi da sauri na gudu kafin fashewar. Motata ta ƙone, wasu mutane sun jikkata, ni ma na samu rauni.

“Amma cikin ikon Allah babu wanda ya rasa ransa,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa motar asibiti ta Sojojin Sama ta zo, inda aka dinga kula da waɗanda suka jikkata, sannan aka ɗauki wasu zuwa asibiti.

A cewarsa jami’an kashe gobara sun isa wajen amma ruwansu ya ƙare, sai da Sojojin Sama suka kai ɗauki sannan suka iya kashe wutar gaba ɗaya.

Wani wanda abin ya shafa, Anthony Ofoke, wanda shi ne mai kula da ayyukan Hukumar Sufuri ta Jihar Ebonyi a Jihar Ribas, ya ce gobarar ta lalata motocinsu guda biyu.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Ribas, SP Grace Iringe-Koko, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce ana ci gaba da bincike don gano musabbabin tashin gobarar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Jaddada Kawo Karshen Bakar Siyasar gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Kan Al’ummar Falasdinu
  • Iran : Hare-haren da Isra’ila ta kai kan Yemen babban laifin yaki ne
  • ISWAP ta yi wa manoma 15 yankan rago a Borno
  • Jami’an tsaro sun daƙile harin Boko Haram sun kashe mayaƙa 5 a Borno
  • Mutum 5 sun jikkata yayin da gidan mai ya ƙone ƙurmus a Ribas
  • Tinubu ya ƙaddamar da jirage 2, ya buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro
  • Cikin makonni kaɗan Obasanjo ya murƙushe Boko Haram — Atiku
  • Ɗaukar fansa: Sojoji sun ragargaji Boko Haram a Dajin Sambisa
  • Mutum 10 sun rasu kan rikicin gona da dabbobi a Filato
  • Mutum 10 sun rasu sakamakon rikicin gona da dabbobi a Filato