A ranar Lahadi Liverpool ta sake matsa ƙaimi a gasar Firimiya bayan ta doke abokiyar karawarta West Ham United ci 2-1 a filin wasa na Anfield dake birnin Liverpool, yayin da Mohamed Salah ya kafa tarihin cin ƙwallaye a kakar wasa ta bana, sakamakon ya sa Liverpool ta samu tazarar maki 13 tsakaninta da Arsenal dake matsayi na biyu a kan teburin gasar.

Yayinda yake saura wasanni shida a kammala gasar, Liverpool na buƙatar maki 3 kacal domin lashe gasar a karo na biyu tun bayan da aka sauya wa gasar suna da fasali, West Ham na matsayi na 17 da maki 35 akan teburin gasar.

Ba Zan Ci Gaba Da Zama A Liverpool Ba -Salah Salah Ya Ƙulla Sabuwar Yarjejeniyar Shekaru 2 Da Liverpool

ESPN ta ruwaito cewa kafin fara wasan, an yi shiru na minti daya a Anfield don nuna girmamawa ga mutane 97 da iftila’i ya rutsa da su a filin wasa na Hillsborough a shekarar 1989, sai dai magoya bayan Liverpool sun ɓarke da ihu jim kaɗan bayan shirun, inda suke nuna jin daɗinsa dangane da sabon kwantiragin shekaru biyu da Salah ya sanya hannu a tsakiyar mako.

A wannan wasan ne Salah ya kafa tarihin wanda ya fi zama komai da ruwanka a wajen zura ƙwallaye a raga a wasannin gasar inda ya zura ƙwallaye 27 ya kuma taimaka aka jefa 18, ana alaƙanta Salah da komawa ƙasashen Larabawa domin cigaba da taka leda, amma kuma sabon kwantiragin da Salah ya sakawa hannu ya sa zai cigaba da zama a Anfield tsawon shekaru biyu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Wang Yi Ya Yi Bayani Kan Ziyarar Shugaba Xi Jinping A Vietnam Da Malaysia Da Cambodia

A yayin wannan ziyara har ila yau, shugaba Xi Jinping ya jaddada cewa, yakin cinikayya zai gurgunta tsarin cinikayyar kasa da kasa, da haifar da mummunan tasiri a kan tattalin arzikin duniya, da tarnake halaltacciyar moriyar kasashen duniya, musamman ma ta kasashe masu tasowa.

 

Sai dai kuma, yayin da ake fuskantar karuwar masu nuna ra’ayin kariyar ciniki a duniya, kasar Sin za ta tsaya kan kokarin tabbatar da ci gaban tattalin arziki, kuma za ta ci gaba da samar da dimbin gudummawa ga yunkurin raya tattalin arzikin duniya, in ji shugaban kasar Sin. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Leicester City Ta Koma Gasar Yan Dagaji Bayan Shan Kashi A Hannun Liverpool
  • NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya
  • KOFIN DUNIYA: Za A Kara Yawan Kasashen Da Suke Bugawa Zuwa 64 A Shekarar 2030
  • Hyda Ghaddar: Mai Son Horar Da ‘Yanmatan Kano Kwallon Kafa
  •  Abbas Arakci: Tattaunawa Da Amurka Ta Hanyar Shiga Tsakanin Oman Ta Shiga Sabon Zango
  • Wang Yi Ya Yi Bayani Kan Ziyarar Shugaba Xi Jinping A Vietnam Da Malaysia Da Cambodia
  • ’Yan sanda sun ceto ɗalibai 10 sun lashe ɗan bindiga a Edo
  • Nijar da Najeriya sun sha alwashin inganta dangantaka a tsakaninsu  
  • Boko Haram Sun Kashe Sojoji 2 Da Wasu A Wani Sabon Hari A Borno
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda a Sambisa da Kudancin Tumbun