A ranar Lahadi Liverpool ta sake matsa ƙaimi a gasar Firimiya bayan ta doke abokiyar karawarta West Ham United ci 2-1 a filin wasa na Anfield dake birnin Liverpool, yayin da Mohamed Salah ya kafa tarihin cin ƙwallaye a kakar wasa ta bana, sakamakon ya sa Liverpool ta samu tazarar maki 13 tsakaninta da Arsenal dake matsayi na biyu a kan teburin gasar.

Yayinda yake saura wasanni shida a kammala gasar, Liverpool na buƙatar maki 3 kacal domin lashe gasar a karo na biyu tun bayan da aka sauya wa gasar suna da fasali, West Ham na matsayi na 17 da maki 35 akan teburin gasar.

Ba Zan Ci Gaba Da Zama A Liverpool Ba -Salah Salah Ya Ƙulla Sabuwar Yarjejeniyar Shekaru 2 Da Liverpool

ESPN ta ruwaito cewa kafin fara wasan, an yi shiru na minti daya a Anfield don nuna girmamawa ga mutane 97 da iftila’i ya rutsa da su a filin wasa na Hillsborough a shekarar 1989, sai dai magoya bayan Liverpool sun ɓarke da ihu jim kaɗan bayan shirun, inda suke nuna jin daɗinsa dangane da sabon kwantiragin shekaru biyu da Salah ya sanya hannu a tsakiyar mako.

A wannan wasan ne Salah ya kafa tarihin wanda ya fi zama komai da ruwanka a wajen zura ƙwallaye a raga a wasannin gasar inda ya zura ƙwallaye 27 ya kuma taimaka aka jefa 18, ana alaƙanta Salah da komawa ƙasashen Larabawa domin cigaba da taka leda, amma kuma sabon kwantiragin da Salah ya sakawa hannu ya sa zai cigaba da zama a Anfield tsawon shekaru biyu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna

Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), ta kama mutane 11 da ake zargi da aikata damfara a Intanet a Jihar Kaduna.

Kakakin hukumar EFCC, Dele Oyewale, ya bayyana cewa an kama waɗanda ake zargin ne a unguwannin Mahuta da Barnawa bayan samun sahihan bayanai game da ayyukansu na yaudara ta yanar gizo.

Yadda Kasar Sin Ta Zo Da Sabon Salon Zamanantar Da Sashen Jigilar Kayayyaki Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Kaso Kusan 80% Sun Soki Musabbabin Barkewar Tarzoma A Amurka

A lokacin da aka kama su, EFCC ta ƙwace wasu kayayyaki daga hannunsu da suka haɗa da mota ƙirar Mercedes Benz C300 mai launin baƙi, wayoyi 14, kwamfutoci guda biyu, iPad, na’urorin mifi guda biyu, lasifikar JBL guda ɗaya, da kuma lasifikar zealot guda ɗaya.

EFCC ta ce za a gurfanar da su gaban kotu da zarar ta kammala bincike.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray
  • Fahimtar Sabon Tunani: Raya Kimiyya Da Fasaha Da Dogaro Da Karfi Na Kashin Kai Sun Ingiza Ci Gaban Kasar Sin 
  • Ƙwazo da juriya suka sa na zura ƙwallaye 10 a wasanni 10 – Mane
  • De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna