Aminiya:
2025-10-22@20:18:44 GMT

Gwamnonin APC sun yi taro a Jihar Kebbi

Published: 17th, October 2025 GMT

Rahotanni sun bayyana cewa Gwamnonin Jam’iyyar APC sun gudanar da wani taron sirri a gidan gwamnati da Jihar da ke Birnin Kebbi.

An bayyana cewa aƙalla gwamnoni 20 daga cikin gwamnoni 24 na jam’iyyar ne suka gudananar da taron ƙarƙashin shugaban ƙungiyar gwamnonin APC, Hope Uzodinma, wanda shi ne gwamnan Jihar Imo.

Gwamnan Gombe ya ƙaddamar da shirin tallafa wa karatun yara mata Wani mutum ya ƙona tsohuwar budurwarsa a Oyo

An bayyana maƙasudin taron gwamnonin kan cewa za su tattauna muhimman batutuwan da suka shafi ƙasa da wasu batutuwa na jam’iyya mai mulkin ƙasar.

Majiyar tashar Channel TV ta ruwaito cewa, shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Nentawe Yilwatda yana Jihar Kebbi amma bai halarci taron gwamnonin ba. A wata sanarwa da aka fitar Nentawe Yilwatda ya ziyarci jihar ne tun a ranar Alhamis.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jam iyyar APC na ƙasa Nentawe Yilwatda

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Jigawa Za Ta Kashe Sama Da Naira Biliyan 2 Wajen Binciken Albarkatun Kasa

Majalisar zartarwa ta jihar Jigawa ta amince da kashe Naira biliyan 2.55 domin gudanar da binciken na musamman, wanda zai mayar da hankali kan albarkatun mai, gas, da sinadarin uranium, tare da cikakken binciken kimiyyar kasa kan ma’adinai a fadin jihar.

A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ya fitar, ya bayyana cewa wannan muhimmin shiri na gwamnatin yanzu babban mataki ne na gaba wajen cika alkawarin gwamnati na ganowa da kuma amfani da albarkatun kasa masu tarin yawa da ke cikin jihar Jigawa.

A cewarsa, wannan bincike zai samar da bayanai masu muhimmanci game da ma’adinai, da mmn fetur da iskar gas da ke karkashin kasa, wanda zai taimaka wajen yanke shawara mai inganci, jawo hankalin masu zuba jari, da kuma tallafawa ci gaban tattalin arziki mai dorewa.

Ya kara da cewa, majalisar ta sake jaddada kudirin gwamnati na bunkasa tattalin arziki ta hanyar bincike da hakar albarkatun kasa bisa tsari da kuma amfani da bayanai na kimiyya.

Sagir ya jaddada cewa, ta hanyar zuba jari a nazarin kimiyyar kasa mai inganci, jihar na da burin samar da sababbin hanyoyin samun kudaden shiga, bunkasa damar samar da ayyukan yi ga matasa, da kuma shimfida tubalin ci gaban masana’antu.

Ya kara da cewa, binciken albarkatun kasa, da mai da iskar Gas zai kasance a hannun kwararrun masana, bisa bin ka’idoji da dokokin kasa da kasa, domin tabbatar da sahihanci, inganci, da amfani mai tsawo na sakamakon da za a samu.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnonin Arewa sun yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a fashewar tanka a Neja
  • Rundunar ‘Yan Sanda A Jihar Zamfara Ta Gargadi Direbobi Game Da Rufe Lambar Mota
  • Jihar Jigawa Za Ta Kashe Sama Da Naira Biliyan 2 Wajen Binciken Albarkatun Kasa
  • Jihar Kwara Ta Ware Naira Biliyan 8 Don Biyan Haƙƙin Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya
  • Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni
  • Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi
  • Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Hanya Akan Kudi Sama Da Naira Biliyan 4
  • Gwamnonin Kano, Katsina da Jigawa sun ƙulla yarjejeniyar bunƙasa wutar lantarki
  • NAJERIYA A YAU: Shin Ya Kamata A Saki Shugaban IPOB Nnamdi Kanu?