Aminiya:
2025-12-07@09:16:12 GMT

Gwamnonin APC sun yi taro a Jihar Kebbi

Published: 17th, October 2025 GMT

Rahotanni sun bayyana cewa Gwamnonin Jam’iyyar APC sun gudanar da wani taron sirri a gidan gwamnati da Jihar da ke Birnin Kebbi.

An bayyana cewa aƙalla gwamnoni 20 daga cikin gwamnoni 24 na jam’iyyar ne suka gudananar da taron ƙarƙashin shugaban ƙungiyar gwamnonin APC, Hope Uzodinma, wanda shi ne gwamnan Jihar Imo.

Gwamnan Gombe ya ƙaddamar da shirin tallafa wa karatun yara mata Wani mutum ya ƙona tsohuwar budurwarsa a Oyo

An bayyana maƙasudin taron gwamnonin kan cewa za su tattauna muhimman batutuwan da suka shafi ƙasa da wasu batutuwa na jam’iyya mai mulkin ƙasar.

Majiyar tashar Channel TV ta ruwaito cewa, shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Nentawe Yilwatda yana Jihar Kebbi amma bai halarci taron gwamnonin ba. A wata sanarwa da aka fitar Nentawe Yilwatda ya ziyarci jihar ne tun a ranar Alhamis.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jam iyyar APC na ƙasa Nentawe Yilwatda

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Dattawan Akpabio ya Nemi Sanata Natasha ta Biya Shi Diyyar Biliyan 200

Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya Godswill Akpabio ya shigar da Sanata Natasha Akpoti ƙara a kotu kan zargin ɓata masa suna yana mai neman ta biya shi diyyar naira biliyan 200.

Sanata Natasha mai wakiltar jihar Kogi ta tabbatar da karɓar sammacin a shafukanta na sada zumunta, inda ta nuna jin daɗinta tana mai cewa ta samu damar bayyana hujjojinta kan zargin yunƙurin lalata da ta zarge shi da yi a baya.

“Yau 5 ga watan Disamban 2025, na karɓi sabon sammacin kotu kan ƙarar diyya ta naira biliyan 200 da Sanata Godswill Akpabio ya kai ni game da ɓata masa suna da zargin lalata,” a cewar Natasha.

“Na yi farin ciki da Sanata Akpabio ya taso da wannan batu saboda kwamatin ɗa’a na majalisa ya ƙi amincewa ya saurare ni kan batun sakamakon matar Akpabio ta shigar da ni ƙara a kotu.”

A watan Fabrairun 2025 ne Natasha ta zargi Akpabio da neman yin lalata da ita bayan rikicin da ya ɓarke a tsakaninsu, wanda ya kai ga dakatar da ita daga zaman majalisar na tsawon wata shida.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudin 2026 a Gaban Majalisa
  • Shugaban Majalisar Dattawan Akpabio ya Nemi Sanata Natasha ta Biya Shi Diyyar Biliyan 200
  • Fyaɗe ga ’yar shekara 12 ya ja wa matashi ɗaurin rai-da-rai a Yobe
  • ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara
  • Iran Ta Mayar Da Martani Kan Sanarwar Bayan Taron  Majalisar Kasashen Yankin Tekun Fasha
  • Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya
  • Iran : Jagora Ya Bayyana Ra’ayin Musulunci Kan Hakkokin Mata
  • Taron IMO : Tehran Ta Yi Watsi Da Zarge-zargen Isra’ila Marasa Tushe