Jihar Jigawa Ta Dukufa Wajen Gina Magudanan Ruwa Domin Kaucewa Ambaliya
Published: 17th, October 2025 GMT
An fara gina magudanan ruwa domin dakile afkuwar ambaliyar ruwa a kananan hukumomin Malam Madori da Kaugama dake jihar Jigawa.
Tawagar Injiniyoyin jihar karkashin jagorancin Daraktan kula da ambaliyar ruwa da zaizayar kasa, Injiniya Mukhtar Muhammad Usman sun ziyarci kananan hukumomin domin duba yadda aikin ke gudana.
Haka zalika Daraktan da mataimakin sa Injiniya Mahdi Isyaku da sauran ma’aikata ssn ziyarci wurin da ambaliyar ruwa tayi ta’adi a garin malam Madori.
A lokacin da tawagar ta fara auna fili da tona magudanun ruwan, daraktan ya ce an fara aikin tona magudanar ruwa mai tsawon kilomita 2 a matsayin wani ɓangare na aikin karkatar da ruwan da ya lalata wurare zuwa sabon wurin da aka tsara.
Yana mai cewar, har ila yau, ana gina wani magudanar ruwa mai tsawon mita 300 a unguwar Gandun Sarki, yayin da aka kammala wasu masu tsawon fiye da mita 390 a Kantamari da kuma mai tsawon sama da mita 500 a Zaburan dake karamar hukumar Kaugama.
Wakilin mazabar Mallam Madori a majalisar dokokin jihar, Alhaji Hamza Adamu Babayaro Malam Madori ya halarci bikin kaddamar da aikin magudanar ruwa mai tsawon mita 2,000 a unguwar Kampala don rage illar ambaliya a yankin.
Shi kuwa shugaban al’ummar Kampala, Ibrahim Zakar, yayi alkawarin samar da masauki ga ma’aikatan domin samun saukin gudanar da aiyukan su don kwalliya da biya kudin sabulu.
A jawabin sa Shugaban karamar hukumar Malam Madori, Alhaji Salisu Sani Garun-Gabas, ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa cika alkawarin da ya dauka a lokacin ziyarar da ya kai yankin, na dakile faruwar ambaliyar da ta lalata gidaje da dama a unguwar Kampala.
Salisu Garun Gabas, ya sami wakilcin mataimakiyar sa ,Hajiya Amina Haruna Dokaje, wacce ta jagoranci kaddamar da aikin tonan magudanar ruwa.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Magudanan Ruwa magudanar ruwa
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Najeriya Ya Mika Sunaye Sabbin Jakadun Kasar su 32 Ga Majalisa Domin Tantancewa
Rahotanni sun bayyana cewa shugaban kasar najeriya Bola Ahmad tunubu ya mika sunayen mutane 32 ciki har da tsohon shugaban hukumar zabe ta kasa mahamud yakubu da tsohon ministan sufurin jiragen sama femi kayode ga majalisar dokokin kasar domin a tantancesu kwanaki bayan tura sunayen mutane 3 a fara da su.
Mai magana da yawun shugaban kasar bayo Onanuga shi ne ya fitar da sanarwa, a cikin wasu wasiku ma banbanta da shugaban kasar ya turawa shugaban majalisa Godswill Akpabiyo ya bukaci majalisar ta amince da sunaye 15 a matsayin jakadun aiki da kuma wasu 17 da bana aiki ba,
Akwai mata guda 4 daga cikin sunayen a matsayin jakadu na aiki da kuma wasu guda 6 a matsayin jakadu ba na aiki ba,
Ana sa ran tura sabbin jakadun a kasashen da najeriya ke da kyakkyawar alaka da su kamar su china, indiya koriya ta kudu , kanada, meziko , hadadiyar daular larabawa, Qatar , Afrika ta kudu, kenya, da kuma kungiyar tarayyar afrika da hukumar UNESCO, kuma zaa sanar da kasar da zaa tura kowannesu da zarar an gama tantancesu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hizbullah Ta Bukaci Shugaban Cocin Katolika Na Duniya Yayi Tir Da Hare-haren Isra’ila November 30, 2025 Iran: Kalaman Da Trump Yayi Na Rufe Sararin Samaniyar Kasar Venuzuwela Ya Sabama Doka. November 30, 2025 Shugaban Pakistan Yayi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Laifukan Yaki Da HKI Ke Tafkawa November 30, 2025 MDD Ta Bukaci Isra’ila Da ta Kawo Karshen Mamayar Da Tayi wa Yankunan Falasdinawa November 30, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 163 November 29, 2025 Iran A Shirye Take Ta Maida Martani Mai Kan Kan Duk Wata Barazanar Tsaro November 29, 2025 Iran Ta Kakkabo Jiragen Yakin HKI Fiye Da 196 A Yakin Kwanaki 12 November 29, 2025 Trump Ya Bada Sanarwan Rufe Sararin Samaniyar Kasar Venezuela Gaba Daya November 29, 2025 Kamfanin Kera Jiragen Sama Na Airbus Ya Bukaci A Dawo Da Jiragen Sama Samfrin A320 Saboda Gyara November 29, 2025 An Kammala Gasar ‘Rayan’ Na AI Ta Kasa Da Kasa A Nan Tehran November 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci