Leadership News Hausa:
2025-10-18@17:25:59 GMT

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

Published: 18th, October 2025 GMT

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

A jawabinsa a wajen taron, Babban Ministan Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ya sanar da wasu shirye-shiyen gwamnatin tarayya da suka hada da sauya wa rumbunan adana amfanin gona kashi 80 zuwa kusa da yankunan da kananan manoma suke a kasar.

“Muna kan yin aiki, domin ganin tabbatar da cewa; mun rage kalubalen karancin rumbunan na adana amfanin gona a Nijeriya,“ in ji Kyari.

Shi ma, a na sa jawabin Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya jaddada muhimmancin shigowar kamfanoni masu zaman kansu cikin fannin, musamman domin samar tsarin aikin noma a fadin kasar mai dorewa.

“Hanya daya tilo da ta dace ita ce, ganin an magance talauci a Arewacin Nijeriya, wannan shi ne ta hanyar zuba hannun jari a fannin, musamman wajen yin noma; domin samun riba,” in ji Sarkin.

Shi kuwa a nasa jawabin, Dakaranta Janar na Bankin AfDB a kasar nan Abdul Kamara, ya jaddada cewa; habaka fannin yin noma domin samun riba a yankin, ta haka ne yankin zai iya cimma burin da ya sanya a gaba na bunkasa fannin aikin noma da kuma dorewar tattalin arzikin yankin.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Noma Da Kiwo Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya October 11, 2025 Noma Da Kiwo Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe October 11, 2025 Noma Da Kiwo Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara October 11, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

Tawagar sun gabatar da kansu ga babban sakataren hukumar gudanarwar ci gaban Jihar Katsina, Dakta Mustapha Shehu. Tawagar sun ce ziyarar wani bangare ne na shirye-shiryen gudanar da aikace-aikace domin inganta zaman lafiya da kuma sanar da tallafin jin kai ga ‘yan gudun hijira.

 

Gwamnan Katsina ya yaba wa Bankin Duniya da ya yi hadin gwiwa da Jihar Katsina don fuskantar matsalolin tsaro da kuma tallafa wa ‘yan gudun hijira.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja October 17, 2025 Rahotonni Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya October 17, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn October 17, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai
  • Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
  • Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu
  • Jigawa Za Ta Kashe Sama Da Naira Biliyan 6 Don Bunkasa Noma, Ilimi Da Kasuwanci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci
  • Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu
  • Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona
  • Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi
  • An Bukaci Manoman Kano Su Shiga Baje Kolin Kayan Noma Na Kasa