Aminiya:
2025-10-17@16:04:29 GMT

Wani mutum ya ƙona tsohuwar budurwarsa a Oyo

Published: 17th, October 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Oyo, ta tabbatar da kama wani mutum mai suna Lawal Faruƙ da ake zargin ya bankawa tsohuwar masoyiyarsa wuta bayan da dangantakar su ta yi tsami.

Majiyar PUNCH Metro ta samu labarin a ranar Alhamis cewa, lamarin ya faru ne a barikin sojoji da ke Ibadan babban birnin jihar.

Jami’an tsaro sun kama ’yan bindiga 2, sun ƙone sansaninsu a Kogi Ba mu ji dadin yi wa mahaifinmu afuwa tare da riƙaƙƙun masu laifi ba – Iyalan Herbert Macaulay

Wani ƙwararre a fagen yaƙi da ’yan tada ƙayar baya, Zagazola Makama wanda ya bayyana yadda lamarin ya faru a shafinsa na sada zumunta na X, ya bayyana cewa, wanda ake zargin ya yi iƙirarin cewa shi da budurwar sun yi rantsuwar cewa ba za su rabu ba.

Sai dai rahoton ya bayyana cewa, wanda ake zargin ya fusata ne bayan da dangantakar ta soyayya da ke tsakaninsu biyun ta lalace.

Lamarin da ya fusata saurayin wanda ake zargin ya zuba wa budurwar man fetur kafin ya banka mata wuta.

Bayan faruwar lamarin, jami’an soji da ke barikin sun ceto matar inda aka garzaya da ita zuwa asibiti kafin su kama wanda ake zargin.

Makama ya rubuta cewa, “Wacce aka kashen mai suna Omolola Hassan, an bada rahoton wanda ake zargin ya zuba mata man fetur sannan kuma ya ƙona ta, wanda aka ce ya fusata ne saboda taɓarɓarewar alaƙarsu.

“A cewar shaidu, jami’an soji da ke barikin sun yi gaggawar shiga tsakani tare da kashe wutar kafin a garzaya da budurwar zuwa asibitin Yawiri da ke Akobo don yi mata magani.

“Wanda ake zargin, wanda ya yi iƙirarin cewa dukkansu sun yi rantsuwar cewa ba za su rabu ba, a halin yanzu yana tsare.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda wanda ake zargin ya da ake zargin ya

এছাড়াও পড়ুন:

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

 

A nata bangare, Sima Bahous ta yabawa ci gaban da Sin ta samu wajen cike gibin fasahohi tsakanin jinsi, da ingiza ci gaban harkokin mata ta kowanne bangare da kare hakkoki da muradun mata.

 

Ta kuma yi kira ga kasa da kasa su hada hannu tare wajen karfafa gwiwar mata da ‘yan mata su samu ci gaba a zamanin amfani da fasahohi. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa  October 14, 2025 Daga Birnin Sin Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin October 14, 2025 Daga Birnin Sin Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya October 14, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an tsaro sun kama ’yan bindiga 2, sun ƙone sansaninsu a Kogi
  • Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara
  • Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya
  • An kama mutum shida yayin da ‘yan sanda suka kubutar da mutane uku da aka yi garkuwa da su a Bauchi.
  • Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano
  • Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani
  • Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta
  • Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kammala Aikin Titin Abuja–Kaduna–Kano Shekara Mai Zuwa