Aminiya:
2025-10-18@16:30:19 GMT

Kamaru: Sojoji da ministoci sun taya ni murnar cin zabe —Issa Tchiroma

Published: 18th, October 2025 GMT

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar adawa a Kamaru, Issa Tchiroma Bakary, ya yi iƙirari cewa ministoci da manyan hafsoshin sojin ƙasar sun taya shi murnar bayan bayyana kansa a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasar da aka kammala.

Issa Tchiroma Bakary ya bayyana cewa ministoci da manyan jami’an tsaron da ministocin sun kira shi a waya suna jaddada goyon bayansu da niyyar biyayya ga kundin tsarin mulkin ƙasar da kuma abin da al’umma suka zaɓa.

Ya bayyana haka ne wani a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, yana mai nuna godiya ga waɗanda suka goyi bayansa, tare da jaddada cewa wannan lokaci yana da muhimmanci matuka ga kasa.

Ya ce, “Ina godiya daga zuciyata ga ministoci da jami’an gwamnati da suka kira ni kwanan nan domin nuna goyon bayansu. Wannan ba lokaci ba ne na wasa ko lissafi — lokacin ne da makomar ƙasa da zaman lafiya ke cikin haɗari, kowa sai ya zaɓi bangarensa, kuma da dama sun riga sun yi hakan,” in ji shi.

Rashin tsaro: An rufe makarantu sama da 180 a Arewa Ma’aurata 136 sun kashe juna a shekara 4

Bakary ya ƙara da cewa wasu manyan hafsoshin soji sun tabbatar masa da cewa suna tare da al’umma, ba tare da la’akari da matsayi ko iko ba.

“Ina godiya ga wasu manyan hafsoshin soji da suka bayyana cewa ba za su ci amanar aikinsu na kare al’umma ba. Ina fatan sauran za su bi sahu nan gaba, domin tarihi zai tuna da waɗanda suka zaɓi al’umma fiye da jin daɗin kansu.”

Ya kuma yi kira ga ’yan jarida da su guji yaɗa labaran karya ko na son zuciya.

“’Yan jarida, kada ku bari a mayar da ku kayan aikin yaɗa labaran da ba su da tushe saboda neman matsayi ko abin duniya. Matasa na kallon ku a matsayin abin koyi — kada ku zama abokan gaba ga al’umma.”

A ƙarshe, Bakary ya yi kira da a haɗa kai da a zauna cikin shiri da kwarin gwiwa.

“Lokaci yana da tsanani, amma  kyakkyawan fata ya fi ƙarfi. Mu tashi tsaye, mu haɗa kai, mu kasance cikin shiri. Makomar ƙasar nan tana hannunmu.”

Sai dai har yanzu hukumar zabe ta Kamaru ba ta fitar da sakamakon zaɓen ba.

Ana sa ran nan da ranar 26 ga watan nan da muke ciki hukumar za ta sanar da sakamakon zaɓen da aka gudanar a ƙarshe makon da ya gabata.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Goyon Baya Issa Tchiroma Bakary Kamaru Zaɓe

এছাড়াও পড়ুন:

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Kura

Kamar yadda rahotanni suka tabbatar, Shugaba Tinubu ya yi wa akasarinsu sassauci ne, bisa rahotannin da ke cewa; wadanda aka yanke wa hukuncin, sun nuna matukar nadama da kuma halin kirki. Haka zalika, ya yafe wa wasu saboda tsufa da samun sabbin fasahohin sana’o’i, ko shiga Jami’ar NOUN. Shugaba Tinubu ya kuma gyara rashin adalcin tarihi, wanda Turawan mulkin mallaka na Burtaniya suka yi wa Sir Herbert Macaulay, daya daga cikin masu kishin kasa a Nijeriya.

 

A takaice dai, kwamitin bai wa shugaban kasa shawara, kan jinkai, karkashin jagorancin babban mai shari’a; kuma ministan shari’a, Prince Lateef Olasunkanmi Fagbemi, ya bayar da shawarar yin afuwa ga fursunoni biyu da 15 da aka yankewa hukunci, wadanda 11 daga cikinsu sun rasu. Kazalika, kwamitin ya ba da shawarar yin afuwa ga fursunoni 82 tare da sassauta hukuncin dauri na fursunoni 65. Fursunonin bakwai da aka yanke wa hukuncin kisa, su ma sun shiga cikin jeren afuwar da shugaban kasar ya yi. Sannan, kwamitin ya ba da shawarar cewa; shugaban kasa ya mayar da hukuncin kisa zuwa daurin rai da rai.

 

Fagbemi ya gabatar da rahoton kwamitin a taron majalisar kasa, wanda shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta.

 

A bangare guda kuma, ‘yan Nijeriya da dama na fadin albarkacin bakinsu, dangane da wannan afuwa da shugaban kasa ya yi wa masu laifukan daban-daban, wasu na da ra’ayin cewa; mafi yawan wadanda aka yi wa afuwar, ‘yan kwaya ne da rikakkun ‘yan ta’adda da kuma wadanda tuni suka mutu. A cikin masu nuna takaicin nasu; akwai tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ‘yan siyasa, masu sharhi kan al’amuran yau da kullum, jam’iyyun adawa da kuma iyalai da sauran abokanan arziki da al’amarin ya shafa.

 

Iyalan marigayi Bilyaminu Ahmed Bello, na daya daga cikin wadanda suka bayyana rashin jin dadinsu, kan afuwar da shugaban kasa ya yi wa Maryam Sanda, wadda aka yankewa hukuncin kisa bisa laifin kashe mijinta, wadanda suka bayyana yin afuwar a matsayin wani mummunan zalinci da aka tafka musu.

 

A wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin da ta gabata dauke da sa hannun Dakta Bello Haliru Mohammed (Dangaladiman Gwandu), a madadin ‘yan’uwa, ‘yan’uwan marigayin sun bayyana matakin da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya dauka na yi wa Sanda afuwa a matsayin wani mummunan sake fama musu raunukan da suka samu da kuma rashin adalci ga dan’uwan nasu.

 

Iyalan Bilyaminun sun bayyana cewa, sun ji matukar takaicin sakin Maryam da aka yi, inda suka bayyana hakan; a matsayin wani yunkuri na dadada wa danginta tare da yin watsi da bacin ran da ya addabi ‘yan’uwa da sauran abokan arzikin marigayin.

 

Maryam, mai shekaru 37, na daya daga cikin mutum 175 da aka yanke wa hukunci, aka kuma yi wa afuwa da jin kai a ranar Alhamis da ta gabata, a karkashin ikon shugaban kasa.

 

A bangare guda kuma, kwatsam! Sai ga sanarwar mahaifin mijin Maryam Sandan cewa; shi da kansa ne ya roki Shugaban Kasa Tinubu, ya yi wa sirikar tasa afuwa.

 

A cewarsa, ya dade yana neman rokon a yi wa Maryam sassauci tare da afuwa, wacce ke fuskantar hukuncin kisa, tun bayan yanke mata hukuncin da aka yi.

 

Alhaji Ahmed Bello Isa, wanda ya bayyana hakan a wata tattaunawa ta hadin gwiwa da aka yi da shi a ranar Talatar da ta gabata a Abuja tare da Alhaji Garba Sanda, mahaifin Maryam, ya bayyana cewa; dalilinsa na yin hakan, saboda tausayi tare kuma son ganin an sako masa surukarsa, domin ta samu ta kula da ‘ya’yanta guda biyu, domin kuwa, kashe ta ba zai taba dawo masa da dansa ba.

 

Ya kara da cewa, “Na yafe wa Maryam da aka samu da laifin kisan dana, kafin a kammala shari’a, na yi iya kokarina na sanar da ‘yansanda da kotu cewa; ba na so a gurfanar da ita a gaban kuliya, domin kuwa jikoki kamar yadda suka rasa mahaifinsu, haka nan kuma za su rasa mahaifiya.

 

“Na dauki wannan a matsayin iftila’i, wanda Allah ya jarrabe ni da shi, a kan abin da ya faru da dana, sannan kuma ko kadan ban ga laifin Maryam ba, amma a lokacin da aka yanke mata hukuncin kisa, addu’a na yi mata tare da rokon Allah ya ji kan ta da rahama, sannan na ce; idan aka kashe ta, wa zai kula da ‘ya’yanta guda biyu? Kawai za su girma ne a matsayin marayu, babu soyayyar uba, babu ta uwa,” in ji shi.

 

Da aka tambaye shi game da maganar da ‘yan’uwa suka yi na nuna damuwarsu kan afuwar da shugaban kasa ya yi mata sai ya ce; “Kowa yana da ‘yancin fadin albarkacin bakinsa a cikin iyalansa, amma a matsayina na mahaifinsa, na yafe mata.

 

Shi ma da yake yin nasa jawabin, Alhaji Garba Sanda, mahaifin Maryam, ya nuna matukar godiyarsa ga Alhaji Bello da sauran daukacin iyalansa, bisa irin halin da suka tsinci kansu a ciki; wanda ba kasafai suke nunawa ba.

 

Iyalan biyu, sun bayyana cewa, sun zabi afuwa, tausayi da kuma imani fiye da ciwon da yake damun su, sannan kuma sun himmatu wajen hada kai; domin renon yaran biyu, cikin kwanciyar hankali da soyayya.

 

Shi ma a nasa bangaren, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, ya zargi Shugaban Kasa Bola Tinubu, da yin amfani da ikon shugaban kasa na jin kai, ta hanyar yin afuwa ga mutum 175, yana mai cewa; matakin “ya gurgunta adalci”, sannan kuma yana da matukar hadari ga rashin bin doka da oda.

 

A cikin wata sanarwa da Atikun ya fitar, ta shafinsa na D a ranar Lahadin da ta gabata ya ce; hakkin yin afuwa, ba yana nufin rashin yin adalci ba ne ko tauye wa wani hakkinsa ba.

 

Har ila yau, Atiku ya soki shigar da mutanen da aka samu da aikata manyan laifuka, yana mai cewa; sakamakon wadanda aka yi wa afuwar, hakan na iya raunana imanin wasu daga cikin mutane tare da karfafawa wasu gwiwa, wajen ci gaba da aikata muggan laifuka.

 

Ya kara da cewa, bai kamata a bar yin afuwa ko jin kai ya hada su jera da aikata muggan laifuka da kuma rage aiwatar da adalci ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa October 16, 2025 Manyan Labarai Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC October 16, 2025 Manyan Labarai Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC October 16, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun tallafa wa mutanen Yobe da N23m bayan harin kuskure
  • Kwamandan Dakarun Sa Kai Na Iran Ya Bayyana Cewa: Iran A Yayin Yaki Da Isra’ila Ta Tarwatsa Wasu Muhimman Wurare 21
  • Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Kura
  • Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa
  • Gwamnatin Kamaru Ta Gargadi Dan Takarar Da Ya Shelanta Kansa A Matsayin Wanda Ya Lashe Zabe
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sanata Ahmed Wadada Aliyu Murnar Ranar Haihuwa
  • Ana Ta Allah Waddai Da Harin Da Aka Kaiwa Al’umma A Jihar Nasarawa
  • Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar
  • Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya