Aminiya:
2025-12-07@10:17:51 GMT

Jami’an tsaro sun kama ’yan bindiga 2, sun ƙone sansaninsu a Kogi

Published: 17th, October 2025 GMT

Jami’an tsaro a Jihar Kogi, sun kama wasu ’yan bindiga biyu da suka ji rauni tare da likitocin bogi da ke yi musu magani.

Hakazalika, sun lalata sansaninsu a lokacin da suka kai musu farmaki.

Ba mu ji dadin yi wa mahaifinmu afuwa tare da riƙaƙƙun masu laifi ba – Iyalan Herbert Macaulay Akwai yiwuwar matsin lamba ya sa Tinubu cire sunayen wasu da ya yi wa afuwa saboda cece-kuce

Mai bai wa Gwamnan Jihar Kogi, shawara kan harkar tsaro, Kwamanda Jerry Omodara (mai ritaya), ya bayyana cewa rundunar haɗin gwiwa da ta ƙunshi sojoji, mafarauta da ’yan sa-kai ne suka kai samamen a garin Aherin-Bunu da ke Ƙaramar Hukumar Kabba-Bunu.

A cewar Omodara, jami’an tsaron sun samu bayanan sirri cewa ana yi wa ’yan bindigar da suka ji rauni magani a wani gida.

Ya ce: “Mun samu bayanai cewa wasu ’yan bindiga biyu da suka ji rauni, ana musu magani a wani gida a Aherin-Bunu.

“Nan da nan muka tura jami’an tsaro, suka kama su tare da likitocin bogi da ke yi musu magani.

“Duk wanda aka kama yana taimaka wa ko yana haɗa kai da masu aikata laifi, za a hukunta shi ba tare da la’akari da muƙaminsa ba.”

Omodara, ya ƙara da cewa jami’an tsaron sun lalata sansanin ’yan bindigar, tare da ƙone wani wani waje da suke amfani da shi a matsayin asibiti da kuma gonakinsu.

Ya gargaɗi jama’a da su guji kowace irin alaƙa da masu laifi, inda ta jadadda cewa gwamnati ba za ta ƙyale duk mai tallafa wa miyagu ba a Jihar Kogi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jami an Tsaro Rauni

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa

Rundunar ’yan sandan jihar Borno ta kama matashin nan da ake zargi da kashe makwabciyarsa a unguwar Shuwari II, a garin Maiduguri babban birnin jihar, ta hanyar daba mata wuka.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:00 na dare a ranar Talata.

Amurka za ta hana ’yan Najeriyar da ake zargi da yi wa Kiristoci kisan kiyashi biza Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwa

Ya ce ana zargin matashin ne mai shekaru 17 da aka fi sani da Amir, wanda makanike ne da kashe matar ta hanyar daba mata wuka.

Wani makwabcin wajen ya shaida cewa ana zargin matashin ne da shiga gidan ta hanyar tsallake katanga bayan ya jira ragowar mutanen gidan sun shiga ciki.

A cewar majiyar, matashin ya ɗauki wuƙa ya daba wa matar gidan, wadda ba a bayyana sunanta ba, a ƙirji da wuya, sannan ya tafi da wayarta da na’urar cajin hannu (power bank).

Majiyar ta ƙara da cewa bayan aikata laifin, wanda ake zargin ya koma gidansu ya wanke tufafinsa da kayan da ya yi amfani da su domin kauce wa bin sahunsa.

Rahotanni sun ce ƙanwar mijin wadda aka kashe ce ta fara sanar da jama’a bayan ta ji ihun matar tana neman taimako.

Lokacin da ta fito ta duba, sai ta ga wanda ake zargin yana gudu ya koma gidansu.

Majiyoyi sun tabbatar da cewa jami’an ’yan sanda sun kama matashin da misalin ƙarfe 2:30 na rana.

Sai dai kakakin rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, bai samu damar yin ƙarin bayani ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nakiya ta hallaka yara 4 a Borno
  • ’Yan bindiga sun harbe ɗan sanda har lahira a Edo
  • Yan Sanda Sun Kama Muhuyi Magaji, Tsohon Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci a Kano
  • Akwai hannun ƙasashen waje a rashin tsaron Najeriya —Sheikh Gumi
  • ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara
  • ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa
  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya