Iyalan marigayi Herbert Macaulay sun soki matakin gwamnatin tarayya na haɗa sunan fitaccen ɗan gwagwarmayar cikin riƙaƙƙun masu laifi a jerin waɗanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wa afuwa bayan ransu.

A wani taron manema labarai da aka gudanar a Legas ranar Alhamis, iyalan tare da goyon bayan dattijo kuma Atona Oodua na Yarabawa, Chief Olabode George, sun bayyana cewa kodayake sun yaba da yadda shugaban ƙasa ya girmama rawar da Macaulay ya taka a tarihin Najeriya, ba daidai ba ne kuma abin ƙasƙanci ne a haɗa shi da wasu da ake tuhuma da manyan laifuka.

Akwai yiwuwar matsin lamba ya sa Tinubu cire sunayen wasu da ya yi wa afuwa saboda cece-kuce Saudiyya ta zaftare wa Najeriya guraban Aikin Hajji da sama da kujeru 28,000

“Idan za a girmama Baba, to a girmama shi ne shi kaɗai,” in ji George a madadin iyalan Macaulay.

Ya ƙara da cewa, “Herbert Macaulay ba barawo ba ne; ya kasance ɗan ƙasa na gari, mai hangen nesa, kuma jikan Bishop Anglican na farko a Afirka. Ya cancanci a ware shi don girmamawa ta ƙasa, ba a haɗa shi da masu laifi ba.”

Daga cikin iyalan da suka halarci taron akwai Erelu Adeola Macaulay, Mr. Lanre Oshodi, Ms. Mayokun Thomas, Miss Kofoworola Macaulay, Miss Adeyinka Macaulay, Mr. Ayo Ogunlana, da Miss Turi Akerele, da sauransu.

A cikin jawabin sa mai taken “Herbert Macaulay: Uban Gwagwarmayar Siyasar Najeriya”, George ya ce gudummawar da Macaulay ya bayar a matsayin ɗan gwagwarmaya, injiniya, da jagoran siyasa har yanzu tana da tasiri.

Ya ce Macaulay ne ya kafa tubalin wayewar siyasar zamani a Najeriya.

“An haifi Herbert Macaulay a shekarar 1864 cikin zuri’ar ilimi, addini da hidima. Da ya so, zai iya yin shiru a tsarin mulkin mallaka, amma sai ya zaɓi ya tsaya tsayin daka wajen adawa da zalunci da faɗa da ƙarya,” in ji George.

Ya bayyana yadda Macaulay ya yi amfani da jaridar Lagos Daily News wajen yaɗa manufofinsa, yadda ya kare Oba Eshugbayi Eleko daga mulkin mallaka, da kuma yadda ya kafa jam’iyyar NNDP a shekarar 1923, jam’iyyar siyasa ta farko a Najeriya.

“Siyasar Macaulay ba ta dogara da gata ba, sai dai manufa. Ya fitar da siyasa daga ɗakunan taron turawa zuwa tituna da kasuwannin tsibirin Legas,” in ji George.

Iyalan da magoya bayansu sun bukaci gwamnati da ta girmama Macaulay ta hanyoyi na musamman, kamar kafa wuraren tunawa da shi, bayar da guraben karatu, da shirye-shiryen horar da matasa bisa ƙa’idodin da ya tsaya kai da fata a kansu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Herbert Macaulay Herbert Macaulay

এছাড়াও পড়ুন:

Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164

164-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka, barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa, shiri wanda yake kawo maku, kissoshi wadanda suka zo cikin Alkur’ani mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Mrtada Muttahari, ko kuma cikin littafan Mathnawa na maulana Jalaluddeen Rumi. Ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu na yau.

////… Madalla, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Al-Haddan dan Aliyu (a) dan Fatimah (s) diyar manzon Allah (s) da muke kawo maku, a cikin shirimmu da ya gabata, mun bayyana yadda Imam Alhassan (a) yay a fita daga Kufa bayan ya karanta wasikar da Kais dan Sa’du dan Ubada ya aika masa bayanda kwamandar rundunarsa kuma dan amminsa Ubaidullahi dan Abbas ya karbi kudi dinari dubu 500 daga wajen mu,awiya ya kuma koma banfarensa ya bar jikin manzon Allah (a).

Mun bayyana  cewa wannan al-amarin ya bakanta ran Imam Al-Hassan (a) amma ya yi hakuri.

Sannan a lokacinda ya fito da rundunarsa zuwa kusa da Mada’in Mu’awiya dan Abu Sufyan ya ci gaba da siyasarsa ta sayan kwamandojojin Imam Al-Hassan,(A), da kuma shuwagabannin kabilun Iraki da suka kasance tare da shi.

Al-Amarin ya kai ga wasu daga cikin shuwagabannin kabilun larabawa sun rubutawa Mu’awiya dan Abusufyan wasika suna fada masa cewa, idan yana so zasu kama Imam Alhassan (a) su mika masa shi, ko kuma su kasheshi idan yana bukatar hakan.

A lokacinda wasikarsu ta isa hannin Mu’awiya dan Abusfyan, ya karantata, sai ya Aikawa Imam Al-Hassan (a) wasikar don ya san cewa bai da magoya baya a cikin kabilun larabawa, sannan yana cikin Hatsari, don kamar yadda suka bayyana a cikin wasikar suna iya kasheshi ko su kama shi su mikawa Mu’awiya ya kasheshi ko kuma ya kasaksantashi.

Sannan mun bayyana cewa, an yi wani lokaci wanda Imam Al-Hassan (a) ya aiki wani dan kabilar Kinda da rundunar mayaka kimani dubu 4 zuwa lardin Amma, sai Mu’awiya ya saye shi da dinari dub u 500, sai ya sulele ya bar rundunar Imam Hassan, kuma koma bangaren Mu’awiya tare da na kusa da shi kimani 200. Imam Al-Hassan (a) ya sake aika wani dana kabilar Murad shi mu’awiya ya saye shi.

Daga nan Imam (a) ya rasa gane wadanda suke tare da shi da gaske da kuma wadanda suka kasance munafukai ne kawai basa tare da shi.

Sannan munce yayi khuduba ga kwamandojojinsa yana fada masu cewa Mu’awiya ba zai cika alkawalin da ya dauka masu idan sun kashe ba, sai duk da haka basu fasa wajen neman yardarm Mu’awiya ba. Inda daga karashe yayi masu Khuduba don ya jarrabasu ya gani, shin suna da niyyar yakar mu’awiya ko dai mafi yawansu yaudara ce.

A cikin khudunar ya nuna masu cewa Mu’awiya ya bijiro masa wani abu, wanda babu daukak babu Daraja a cikinsa. Sannan ya tambayesu idan suna son rayuwa zai amice da bukatar idan kuma sun sun shiryawa mutuwa to a shirye yake su fara yaki da Mu’awiya har sai Allah ya hukunta a tsakaninsu. A nan sai mafi yawan mutane sun bukaci ya amince da sulhu don suna sun rayuwa.

Daga nan Imam Al-Hassan ya tabbatar da cewa, ko ya shiga yaki da Mu’awiya to yana yaki ne ba tare da yana da mataimaka ba.

Sannan ya fahinci cewa idan ha rya jinkirta sulhuntawa da Mu’awiya dan Abu sufyan to kuma wadannan da suke tare da shi zasu kamashi su mikawa Mu’awiya ko kuma su kashe shi.

Sannan ya san cewa idan ya shiga hannun mu’awiya zai wulakantashi matuka ya kuma kasheshi idan ya ga dama.

 Zaidu dan Wahab Aljahni Aljahani ya shi wajen Imam (a) kafin sulhu da mu;awiya ya ruwaito yadda Imam Al-Hassan (a) ya gaji da mutanen kufa ya kosa da su, yana son fita daga cikinsu idan zai sami dama yin hakan. Yace na shga a wajen Imam Al-Hassan(a) a Madi’an yana jinyar cinyarsa da aka daba masa wuka a kanta, sai n ace masa: Ya dan manzon Allah mutanen a rikice suka? . sai ya masa da cewa

 (Ai ni ina ganin Mu’awiya ya fi mana alkhairi a kan wadannan mutane, wadanda suna riya cewa su Mabiya nane amma suna neman kashe ni, sun yi wawason dukiyata sun kuma kwace kudina, wallahi in samu amana daga Mu’awiya don in kare jinina, da na iyalan gidana da Mabiya na ya fi mani a kan su kashe ni, iyalan gidana su lalace. Kuma da na yaki mu’awiya da sun kama wuyata sun mika ni gareshi ba tare da yaki ba.

Na rantse da Allah in amince da sulhu da shi ya barni da mutunci na, ya fi mani da ya kasheni ina fursnina yaki a hannunsa. Ko kuma ya gafartamani, wannan ya kasance abin kunya ne ga Banuhashin har abada. Da kuwa Mu’awiya ba zai gushe ba yana mani gori da shi, hakama yayansa a kan rayayye da matacce daga cikimmu. )

Bayan wadan nan abubuwan da suka faru, imam y afara tuninan makomar al-ummar musulmi idan sun shiga hannun Mu’awiya dan Abusufyan, musamman tashe-tashen hankula da zasu faru, su kuma rikita harkokin shugabanci a cikin daular kakakan. Yana tunanin makomar iyalan gidan manzon Allah (S) da tsirarin shi’arsu idan Mu’awiya ya karbi iko da daular musulunci.

Yana tunan makamar Mabiya iyalan gidan manzon Allah tsiraru wadanda suka rage a cikin rundunarsa, da kuma sahabban Amirulmuminina yan kadan da suka rage.

Yana tunanin irin mummunan halin da zasy fada ciki, idan Mu’awiya ya karbi iko da daular Musulunci.  Yana tunanin menene makomar addinin kakakinsa manzon Allah (s) idan Mu’awiya ko Banu umayya suka karbi iko da daular musulunci.

Wannan al-amari mai ban tsaro ne kwarai da gaske, kuma yana tunani Mu’awiya dan Abusufyan zai sauya al-amura da dama a cikin addinin musulunci, wanda zai kara rikita addinin a cikin musulmi da kuma wadanda zasu zo nan gaba.

Don haka al-amarin yana bukatar tunani mai zurfi da kuma daukar matakan da suka dace.  Amma daga karshe a tsaida cewa maslah ga Musulunci da Musulmi shi ne sulhuntawa ga Mu’awiya dan Abu Sufyan, sannan ya kama aiki yada addinin musulunci na gaskiya ta wasu hanyoyin, da kuma nuna turjiya ga bukatun Mu’awiya na shafe addinin kakansa manzon Allah (s) daga doron kasa.

Malaman tarihi sun yi sabani kan dalilan da suka sa Imam Al-Hassan(a) ya sulhunta da Mu’awiya dan Abu sufyan da kuma lalurar da ta sa ya sulhunta da shi. Daga cikinsu Assafiy ana cewa, lalle an samu wasu shuwagabannin a bayana wadanda suka bar shugabanci, suka kuma tube shugabanci suka barwa wasu don maslahar addini da kuma musulmi. Daga cikinsu ya ambaci Imam Al-Hassan(a) Almujtaba(a).

Yace Imam Al-Hassan ya cewa Mu’awiya Lallai akwa basussuka a kan na, ka biya mani wadan nan basussuka ka je da Khalifancin, sai suka biya masa basussukansa ya barmasu khalifanci.

Amma gaskiyar Al-Amarin ba haka bane, Imam Hassan (a) bai saida Khalifanci da basussukan da Mu’awiya ya biya masa ba. Muna neman tsari daga Allah da wannan Magana da Assafadi.

Sai kuma dalilanda suka sa sojojin Imam Al-Hassan (a) suka kasa samun nasara a kan sojojin Mu,awiya, daga cikinsu akwai.

Faduwar kwamandojin  sojojin Imam (a) karkashin kudaden Rashawa da Mu’awiya wanda ya sa spjpjinsa suka suka yi Rauni, suka kuma kasa tunkarar sojojin Mu’awiya, kuma a cikin manya-manyan kwamandojojin sojojin Imam da suka karbi rashawa suka kuma koma bangaren Mu’awiya shi ne, Ubaidullah dan Abbas wand abanda kudaden da ya karba a wajen Mu’awiya ya tafi da sojojin Imam Alhassan (a) har dubu 8000.

Dalili na biyu shi ne cewa, akwai wasu kungiyoyi manya-manya a cikin sojojin Imam Al-Hassan (a) wadanda basa son daular Ahlulbaiti (a) ko daular Hashimawa,  don haka sai suka zama suna neman daman da zasu kifar da daular kuma sune Khawarijawa da kuma shuwagabannin kabilu wadanda suka zama jasusun Mu’awiya a cikin sojojin Imam (a). Su suke aika masa sakonni dangane da halin da ake ciki a cikin kasar Iraki da kuma sojojin Imam Al-Hassan.

Khawarijawa tare da akidarsu ta cewa khalifan musulmi dole ne ya kasance mai bin akidarsu, wannan yasa da’iman suna cikin fada da shugaba wanda baya cikinsu. Hakama wadan nan shuwagabannin kabilun larabawa mutane ne masu kyadayin duniya ba abinda zai wadatar da su sai su zama shugabannni, idan ba haka ba bu Ruwan kabilunsu da duk wanda yake shugabancin ko yake da iko.

Sannan mafi yawansu basu san addini ba, don haka ba sa biyayya da kowa sai shugaban kabilarsu. Wannan kuma shi ne tsarin jahiliyya kafin zuwan addinin musulunci.

Wannan ya nuna cewa bayan manzon Allah (s) larabawa da dama sun fi girmama kabilarsu a kan addini a wani lokaci. Sannan abi  mamaki shi ne, suna daukar shuwagabannin Ahlulbaiti suna neman girma wa kabilarsu ko danginsu Banu Hashin ne. Alhali Ahlul baita (a)shuwagabanni ne  wadanda Allah ya zaba kamar yadda ya zabi manzon Allah (s), don haka ba wanda zai taba zama dai-dai da su.

Sannan wani Abu wanda ya kashe guiwar rundunar Imam Al-Hassan (a) shi ne rashin samun ganimar yaki. A dukkan yake-yaken da musulmi suka yi a zamanin Amirul muminina Aliyu dan Abitalib (a), Jamal Siffin da kuma Nahrawan  yake-yake ne tsakanin musulmi. Wanda babu ganima a cikinsa sai abinda aka samu na kayakin yaki.

Wannan ya sa da dama daga cikin mayaka wadanda suka kasance tare da shi basa samun dukiya mai yawa da ganima da suka saba samu a zamanin manzon Allah (a) da kuma khalifofi uku da suka biyu bayansa.

Sai dan a nan Allah ba musanya masu da adalcin Amirul muminina (a) ta yadda a cikin shekaru kimani 5a da ya yi a matsayin shugaban daular musulunci ya sami nasara shafe talaunci a dukkan yankunan da ke karkashin ikonsa.

A lokacin babu wani musulmi da yake kwana da yunwa, ko wanda yake cikin talauci mai tsanani. Amma shuwagabannin kabilun larabawa suna da gurin tara dukiya ne shi yada basu wadatu da adalcin Imam Ali (a) ba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Baqaei: Amurka Ce Babbar Barazana Ga Zaman Lafiya Da Tsaro A Duniya December 1, 2025 Paparoma Leo Na 14 Yana Ziyarar Aiki Na Kwanaki 3  A Kasar Lebanon December 1, 2025 Wani Dan Adawa Da Gwamnatin Paul Biya Ya Mutu A Gidan Yari A Kasar Kamaru December 1, 2025 Tawagar ECOWAS Ta Bar Guinea – Bissau bayan da shugaban kasar yayi barazanar korarsu Da Karfi December 1, 2025 Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100% December 1, 2025 Gaza: Fiye da Falasdinawa 350 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila tun bayan tsagaita wuta December 1, 2025 Hamas : Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta December 1, 2025 Nijar : zamu sayar da uranium dinmu ga wanda muka ga dama_ Janar Tiani December 1, 2025 Tawagar ECOWAS za ta je Guinea-Bissau, bayan juyin mulkin soji December 1, 2025 Ministan Harkokin Wajen Turkiya Ya Isa Birnin Tehran Kuma Ya Gana Da Takwaransa Na Iran December 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • Zanga zanga Ta Barke A Isra’ila Yayin Da Natanyaho Ke Neman Afuwa Kan Batun Cin Hanci Da Rashawa
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 163
  • Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo
  • Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe
  • Yadda ’yan mata ke kuɗancewa da kasuwancin fara a Kano
  • Yadda ’yan mata ke kufancewa da kasuwancin fara a Kano
  • Asibitin Kula Da Masu Lalurar Ƙwaƙwalwa Na Kaduna Na Bunƙasa Ta Fannoni Daban-Daban