Aminiya:
2025-10-17@11:48:29 GMT

’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 8 a harin kwanton ɓauna a Zamfara

Published: 17th, October 2025 GMT

Aƙalla jami’an tsaro takwas, ciki har da ɗan sanda guda ɗaya da masu tsaron al’umma bakwai, sun rasa rayukansu a wani harin kwanton bauna da aka kai musu a hanyar Gusau–Funtua da ke Jihar Zamfara a ranar Alhamis.

Lamarin ya faru ne a lokacin da gamayyar jami’an tsaro, waɗanda suka haɗa da ’yan sanda da mambobin rundunar tsaro ta jihar Zamfara ke amsa kiran gaggawa daga kauyen Tungawa da ke ƙaramar hukumar Tsafe.

An ceto mutane 3 da aka yi garkuwa da kama wasu a Bauchi Majalisar Dattawa ta amince da Amupitan Shugaban INEC

“Maganar da nake yanzu haka, an kwashe gawarwakin jami’an da suka mutu zuwa Gusau domin jana’iza,” in ji wani shaida da aka bayyana sunansa da Tsafe.

Shugaban ƙaramar hukumar Tsafe, Hon. Garba Fanchan, ya tabbatar da faruwar lamarin tare da miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu.

Ya bayyana harin a matsayin “mugunta da rashin imani,” yana mai tabbatar wa jama’a cewa gwamnati na ɗaukar matakan gaggawa don dakile matsalar tsaro da ke ƙaruwa a yankin.

Gwamnan jihar, Dauda Lawal, shi ma ya aike da saƙon ta’aziyya ga iyalan mamatan.

A cikin wata sanarwa ranar Alhamis, gwamnan ya jajanta wa hukumomin tsaro tare da addu’ar Allah ya gafarta wa jami’an da suka rasa rayukansu.

“Waɗannan jaruman sun mutu ne a yayin da suke bakin aiki don kare al’ummarmu. Allah ya gafarta musu, ya sa sun huta,” in ji Gwamna Lawal.

Hanyar Gusau–Funtua na ƙara zama wurin da ake yawan kai hare-hare, inda rahotanni ke nuna cewa kusan kowace rana ’yan bindiga na kai farmaki ga matafiya a hanyar.

Hukumomi sun sha alwashin ƙara daukar matakai domin dawo da zaman lafiya a hanyar da kuma tabbatar da lafiyar matafiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

Wani daga cikin waɗanda suka ji rauni, wanda shi ne mai kuɗin, ya gode wa jami’an FRSC bisa gaskiya da amana da suka nuna, yana mai cewa abin koyi ne ga kowa.

FRSC ta gargaɗi direbobi da su riƙa kula da motoccinsu akai-akai tare da bin ƙa’idojin hanya domin guje wa aukuwar haɗura.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato October 16, 2025 Manyan Labarai Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson October 16, 2025 Labarai Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari  October 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma
  • Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika
  • Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara
  • ’Yan sanda sun kama gungun masu fashi a kan hanyar Katsina zuwa Kano
  • Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina
  • Ana Ta Allah Waddai Da Harin Da Aka Kaiwa Al’umma A Jihar Nasarawa
  • Ba za mu yi sulhu da ’yan bindiga ba sai sun yi tuba na gaskiya — Radda
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 1, sun sace dabbobi a Katsina
  • ‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako