Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya
Published: 17th, October 2025 GMT
Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, ya bi sahun dan rajin kare hakkin dan adam kuma tsohon dan takarar shugaban kasa, Omoyele Sowore, wajen yin kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta sakin jagoran kungiyar Biafra (IPOB) Nnamdi Kanu.
A cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na D, Atiku, ya bayyana ci gaba da tsare Kanu a matsayin “rashin girmama bin doka a Nijeriya.
Kanu dai, na fuskantar tuhumar ta’addanci ne da cin amanar kasa da kuma nuna tunzura a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja, wanda kuma a lokuta da dama yake musanta hakan. Har ila yau, ya kasance a tsare tsawon shekaru duk da hukuncin da kotu ta yanke na bayar da umarnin a sake shi.
Atiku, tsohon dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, ya bayyana cikakken goyon bayansa da fafutukar da Sowore ke yi na ga nin an saki Kanu.
Da yake yin jawabi a wajen taron, Kwamared Gamji ya bayyana cewa; “Mun zo nan ne, domin mu nuna fushinmu da rashin amincwar mu da kuma nuna wa duniya cewa, ba ma tare da ‘yan siyasa masu neman mulki ido rufe a Nijeriya, wadanda ke son yin amfani da tsare Nnamdi Kanu wajen tayar da zaune tsaye a kasar.
“Tsohon dan takarar shugaban kasa kuma mamallakin gidan jaridar Sahara Reporter, Mista Omoleye Sowore, da babanmu, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, na shirin shirya wani gangamin taro, domin sakin Nnamdi Kanu.
Ya kara da cewa, mun ji wannan sanarwa tasu, sannan kuma ba ma tare da su. “Saboda son rai irin naku, kuna so ku yi amfani da jinin matasan Nijeriya, wajen cimma burinku,” in ji Gamji.
“Babban kuskuren da za su tafkawa shi ne, ranar da za su fito, ita ce ranar da matasa sama da miliyan 63, wadanda jiga-jigan matasan Arewa ne; su ma za su fito tare da rokon Shugaba Ahmed Bola Tinubu, da ya ci gaba da gudanar da kyawawan ayyukan da sanya a gaba.
Kwamared Gamji ya kara da cewa, “Za mu mamaye dukkannin titunan Abuja, daga ranakun 20, 21 zuwa 23 ga watan Oktoba, domin nuna goyon bayanmu ga Shugaba Tinubu”.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Labarin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Najeriya ƙarya ne – Sarkin Musulmi
Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, ya karyata zargin kisan kiyashi ga Kiristoci a Najeriya, yana mai cewa wannan ikirari ƙarya ne kuma bai kamata a ci gaba da yada shi ba.
Sarkin ya bayyana hakan ne a taron Babban Majalisar Sarakunan Gargajiya na Arewa na shekarar 2025, wanda aka gudanar a Birnin Kebbi, Jihar Kebbi, a ranar Talata, da taken: “Ƙarfafa Haɗin Gwiwar Al’umma Domin Samun Zaman Lafiya da Tsaro Mai Dorewa a Arewa.”
Masu kwacen waya sun kashe ma’aikaciyar lafiya a Zariya Majalisa ta soma binciken yadda aka kashe $4.6bn na tallafin kiwon lafiyaYa ce: “Sun dade suna cewa ana kisan kiyashi ga Kiristoci a Najeriya daga ƙasashen Yamma kamar Amurka, Kanada da sauransu. A ina? Yaushe? Wannan labari ne na ƙarya.”
Sarkin, wanda kuma shi ne Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya na Arewacin Najeriya ya ce ba zai yiwu a ce ana irin wannan kisa a wani yanki na Najeriya ba, kuma sarakunan gargajiya ba su sani ba.
Ya roƙi shugabannin ƙasa da su sanya dokoki kan amfani da kafafen sada zumunta saboda illar da suke haifarwa da kuma abubuwan batanci da ake wallafawa game da ƙasa da mutane a cikinsu.
Sarkin ya kuma buƙaci ‘yan Najeriya da su daina zagin sojoji, yana mai jaddada cewa da babu sadaukarwarsu, da ƙasa ba za ta ci gaba da kasancewa ƙasa ɗaya mai zaman lafiya ba.
Sai dai ya amince cewa sojoji na fama da ƙalubale da gazawa, amma ya soki maganganun da ake yi a kafafen sada zumunta da ke zargin jami’an tsaro da haɗin gwiwa da ‘yan ta’adda, yana mai cewa hakan rashin tausayi ne kuma bai dace ba.
Sarkin ya sake jaddada goyon bayan sarakunan gargajiya ga ci gaban dimokuraɗiyya da biyayya ga dukkan shugabannin da aka zaɓa, ciki har da Shugaban Ƙasa, Majalisun Tarayya da na Jihohi, da Gwamnoni.
Ya kuma buƙaci sarakunan da suka halarci taron da su haɗa kai domin fuskantar ƙalubalen da ƙasa ke ciki, yana mai cewa za a mika shawarwarin da suka bayar ga Gwamnonin Arewa domin ɗaukar matakin da ya dace.
Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu a taron ya ce sarakunan gargajiya na da muhimmiyar rawa wajen inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali.
Ya ce suna da ƙwarewa wajen rage tashin hankali, warware rikice-rikice, da kawo zaman lafiya a lokacin ƙalubale.