Farfesa Jibril Amin Likita kuma tsohon malamin Jami’a, ya rasu a jiya  Laraba yana dan shekara 85 a duniya.

Jaridar Daily Trusta ta Najeriya ta nakalto majiyar iyalar mamacin na tabbatar da haka. Ta kuma bayyana cewa kwamishin gidaje a jihar Adama Hon Abdullahi Prambe ya tabbatar da labarin. Sannan ya kara da cewa an yi masa sallar Jana’iza a babban masallacin kasa a Abuja a yau Alhamis.

Sannan za’a maida shi garinsa Song na jihar Adamawa inda za’a rufe shi.

A rayuwarsa dai Farfesa AAmin likitan zuciya ne, sannan malami da shugaba Jami’ar Maiduri na Jahar bornin a wani lokaci, ya kuma karantar. Har’ila yau Farfesa Amin ya rike kujerar Ministan ilmi da manfetur, sannan jakadan Najeriya A Amurka sannan yan majalisar dattawa mai wakiltan Adama ta tsakiya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

A bana ake bikin cika shekaru 50 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da kungiyar Tarayyar Turai ta EU, ana kuma daf da gudanar da sabon zagayen taron jagororin Sin da EU. Sakamakon hakan, jerin ayyukan cudanya a matsayin koli tsakanin sassan biyu na kara jan hankali.

A baya-bayan nan, an gudanar da dandalin tattaunawa na manyan jami’ai tsakanin Sin da EU karo na 13 a birnin Brussels na kasar Belgium. Kuma ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gana da shugabannin EU, tare da ziyartar kasashen Jamus da Faransa. Bangaren Sin ya jaddada cewa, bunkasar tafarkin ci gaban alaka tsakanin Sin da EU ya nuna kyakkyawar dangantakar sassan biyu maimakon adawa da juna, kuma hadin gwiwarsu shi ne tushen cimma nasara tsakaninsu. Kazalika, ya yi kira ga Sin da EU da su hada karfi waje guda don samarwa duniya wani yanayi na tabbaci.

Ya ce, matsayin alakar Sin da EU na manyan karfi biyu, kuma manyan kasuwanni biyu, kana manyan wayewar kai biyu, ya shaida damar musaya da hadin gwiwa, ba gare su kadai ba, har ma da dukkanin duniya baki daya. Jimillar karfin tattalin arzikin Sin da EU ya haura daya bisa ukun na duniya baki daya, kana darajar yawan cinikayyarsu ta haura daya bisa hudun ta duniya baki daya. Sassan biyu na rike da manufar cudanyar mabambantan sassa, suna goyon bayan cinikayya marar shinge, da wanzar da tattaunawa da tsare-tsaren gudanarwa kan muhimman batutuwa, irinsu sauyin yanayi da fasahohin AI. A halin da ake ciki, rikicin siyasar yankuna na kara tsananta, an kuma shiga yakin haraji da na cinikayya. Sin da Turai na da nauyi da hakki, da ikon hada hannu waje guda don kare adalci, da nuna adawa da cin zali daga bangare guda, da nuna kin jinin baiwa kasuwa kariya. Kamar dai yadda Sin ta bayyana, idan Sin da Turai sun wanzar da tattaunawa da hadin gwiwa, zai yi wuya a kai ga yin fito-na-fito tsakanin wasu sassa. Kazalika, idan Sin da Turai sun zabi bude kofa, da hadin gwiwar cimma moriya tare, hakan zai sauya salon dunkulewar tattalin arzikin duniya. Idan Sin da Turai sun hada hannu wajen aiwatar da manufar cudanyar mabambantan sassa, duniya ba za ta tsuduma cikin yanayi na hargitsi ba. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Fira Ministan Pakistan Tare Da Tattaunawa Kan Harin Da Iran Ta Fsukanta
  • Ayatullahi Khatami Ya Ce Hukuncin Da Ya Cancanci Trump Da Netanyahu Shi Ne Kisa Saboda Zubar Da Jinin Bil’Adama
  • NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya
  • SON Ta Bada Shaidar Ingancin Kayayyaki Ga Wasu Kamfanoni A Kaduna
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Harin Kan Cibiyar Makamashin Nukiliya Cin Amanar Diflomasiyya Ce
  • Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota
  •  Arakci Ya Mayar Wa Da Jami’ar Harkokin Wajen ” EU” Martani
  • ‘Mutum 600 da suka bace a ambaliyar Mokwa sun mutu’
  • NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya Fuskanta