Amurka ta sake yin watsi da kiran tsagaita a wuta Gaza
Published: 5th, June 2025 GMT
Amurka ta sake hana kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya kiran tsagaita bude wuta da kuma kai agajin jin kai a Gaza.
Wannan hawa kujerar na-ki shi ne irinsa na farko na sabuwar gwamnatin Trump kuma yana zuwa ne a daidai lokacin da Isra’ila ke fuskantar matsin lamba daga kasashen duniya kan ci gaba da yakin da takeyi a gaza dama hana shigar da kayan agaji.
Daftarin kudurin da aka gabatar wa kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya a ranar Laraba ya bukaci “a gaggauta tsagaita wuta na dindindin” da kuma sakin wadanda aka yi garkuwa da su ba tare da wani sharadi ba.
Kudirin da kasashe 10 wadanda ba mambobin kwamitin na dindindin ba suka gabatar, ya samu sahalewa daga kasashe 14, yayin da Amurka ta yi fatali da shi.
Kafin kada kuri’ar, Amurka ta ce “kudirin zai wargaza kokarin diflomasiyya na cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta gaskiya, kuma zai karfafa wa Hamas,” ne in ji jakadiyar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya, Dorothy Shea.
Jakadan Falasdinawa a Majalisar Dinkin Duniya Riyad Mansour ya bukaci MDD da ta dauki mataki.
Wannan matakin na ranar Laraba ya kasance karo na shida da Amurka ke toshe kudurin tsagaita wuta a Gaza tun watan Oktoban shekarar 2023.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a Majalisar Dinkin Duniya
এছাড়াও পড়ুন:
Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara
Wata kotu a kasar Amurka ta yanke wa wasu ’yan Najeriya su biyar hukuncin daurin shekaru 159 bisa samun su da da laifin damfarar Amurkawa sama da 100.
Kotun dai ta sami mutanen ne da laifin damfarar kamfanoni da hukumomin gwamnatin kasar kudin da yawansu ya kai Dala miliyan 17, kwatwankwacin Naira biliyan 27 da miliyan 200.
Hakan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sashen shari’a na kasar ya wallafa a shafinsa na intanet ranar Laraba, mai dauke da sa hannun mai rikon mukamin Babban Lauyan gwamnati na gundumar gabashin Texas, Ray Combs.
’Yan bindiga sun kashe manoma 24 a Katsina Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a ZamfaraSanarwar ta ce mutanen da aka yanke wa hukuncin sun hada da Damilola Kumapayi, Sandra Iribhogbe, Edgal Iribhogbe, Chidindu Okeke and Chiagoziem Okeke, kuma mambobi ne a wani gungun ’yan damfara na kasa da kasa.
Lauyan ya ce ’yan damfarar sun fara harkallar ne tun a shekara ta 2017, inda suke hakon tsofaffi da kuma masu rangwamen gata ta hanyar kirkiro dabaru daban-daban na karbar kudi daga wajensu, wasu lokutan ma ilahirin abin da suka tara a rayuwarsu.
“Da zarar sun karbi kudade daga mutane ta hanyar damfarar, sai su tuttura su ta hanyar asusun ajiya a bankuna da dama da kuma abokan harkallarsu da ’yan kasuwa da ke kasashe a nahiyoyin Afirka da Asiya,” in ji lauyan na gwamnatin Amurka.
Sanarwar ta ce bayan kama su, an gurfaran da su a gaban kotu kan laifukan da suka hada da hadin baki, zambar kudade da kuma damfara, wadanda dukkansu suka amsa aikatawa.
A cewar sanarwar, hakan ce ta sa alkalin kotun, Mai Shari’a Amos Mazzant, ya yanke musu hukuncin daurin shekaru daban-daban a kurkuku.