HausaTv:
2025-12-10@13:45:51 GMT

Amurka ta sake yin watsi da kiran tsagaita a wuta Gaza

Published: 5th, June 2025 GMT

Amurka ta sake hana kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya kiran tsagaita bude wuta da kuma kai agajin jin kai a Gaza.

Wannan hawa kujerar na-ki shi ne irinsa na farko na sabuwar gwamnatin Trump kuma yana zuwa ne a daidai lokacin da Isra’ila ke fuskantar matsin lamba daga kasashen duniya kan ci gaba da yakin da takeyi a gaza dama hana shigar da kayan agaji.

Daftarin kudurin da aka gabatar wa kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya a ranar Laraba ya bukaci “a gaggauta tsagaita wuta na dindindin” da kuma sakin wadanda aka yi garkuwa da su ba tare da wani sharadi ba.

Kudirin da kasashe 10 wadanda ba mambobin kwamitin na dindindin ba suka gabatar, ya samu sahalewa daga kasashe 14, yayin da Amurka ta yi fatali da shi.

Kafin kada kuri’ar, Amurka ta ce “kudirin zai wargaza kokarin diflomasiyya na cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta gaskiya, kuma zai karfafa wa Hamas,” ne in ji jakadiyar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya, Dorothy Shea.

Jakadan Falasdinawa a Majalisar Dinkin Duniya Riyad Mansour ya bukaci MDD da ta dauki mataki.

Wannan matakin na ranar Laraba ya kasance karo na shida da Amurka ke toshe kudurin tsagaita wuta a Gaza tun watan Oktoban shekarar 2023.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a Majalisar Dinkin Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas, ta yi maraba da bayannan cewa an cire sunantsohon firaministan Burtaniya Tony Blair daga wadanda ake tunanin zasu jagoranci Gaza a shirin zaman lafiya na shugaban Amurka Donald Trump a Gaza.

Jaridar Financial Times ta ruwaito a ranar Litinin cewa kasashen Larabawa da na Musulmi ne suka nuna adawa da shigar da M.Blair cikin “hukumar rikon kwarya” da Trump ya bayyana a matsayin wani bangare na shirinsa na zaman lafiya a Gaza.

Tony Blair ya sha suka a faɗin duniyar Musulmi saboda rawar da ya taka a mamayar da Amurka ta jagoranta a Iraki a shekarar 2003, wanda daga baya aka gano cewa kawai zarge-zargen karya ne.

Wani Jami’in Hamas, Taher al-Nunu, ya ce rahotannin yiwuwar cire Blair ya yi daidai da kiran da kungiyar ta yi ga masu shiga tsakani don hana shi shiga kowace hukuma da ke da alaka da Gaza.

A daya bangaren kuma Al-Nunu ya sake nanata cewa ƙungiyar ta kasance “a shirye don tsagaita wuta na dogon lokaci” muddin gwamnatin Isra’ila ta amince da dukkan sharuddan tsagaita wuta, wani abu da Tel Aviv ta kauce masa zuwa yanzu ta hanyar karya yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma a farkon watan Oktoba.

Jami’in na Hamas ya kuma jaddada cewa duk wani shiri da ya shafi rundunar ƙasa da ƙasa da aka ɗora wa alhakin kwance damarar yaƙi da ƙungiyoyin gwagwarmaya da ƙarfi, “an yi watsi da shi kuma ba a taɓa tattauna shi ba.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon December 9, 2025 Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine December 9, 2025 Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba December 9, 2025 Najeriya : Matsala ce ta sa jirgin sojinmu yin saukar gaggawa A Burkina Faso December 9, 2025 Saudiya da Qatar Zasu Gina Layin Dogo Mai Sauri Tsakanin Kasashen Biyu December 9, 2025 Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki December 9, 2025 Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan  Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko  Da  ‘Yan Ta’adda December 9, 2025  Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha December 9, 2025 An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa” December 9, 2025  Talauci Yana Karuwa A “Isra’ila” Bayan 7 Ga Watan Oktoba December 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya
  • Majalisar Dattawa Ta Bawa Tunubu Damar Kai Sojoji Zuwa Kasar Benin
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin
  • Iran da Saudiyya sun sake jaddada fadada dangantakarsu
  • RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne
  • An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza
  • Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon
  • MِِِِDD:  Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso
  • Tawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini