Aminiya:
2025-04-30@23:24:52 GMT

Akwai ’yan ƙwaya a cikin sarakunan gargajiya — Obasanjo

Published: 16th, March 2025 GMT

Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya nuna damuwarsa kan yadda sarautar gargajiya ke rasa martabarta a ƙasar nan.

A cikin sabon littafinsa mai suna ‘Nigeria: Past and Future’, ya bayyana cewa yanzu akwai masu laifi, ’yan daba, da masu safarar miyagun ƙwayoyi da suka zama sarakuna a wasu yankuna na Najeriya.

Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga Amurka Trump ya dakatar da kafar watsa labarai ta VOA

“A yau, akwai ’yan daba, masu safarar miyagun ƙwayoyi, ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane da ake kira sarakuna,” in ji Obasanjo.

“Wannan abu ne mai matuƙar ban takaici, kuma yana daga cikin matsalolin da ke addabar Najeriya.”

Ya ce dole ne a dawo da mutunci da ƙimar sarautar gargajiya domin tana taka rawar gani a ci gaban ƙasa.

Har ila yau, ya gargaɗi shugabanni cewa idan ba su magance matsalolin da jama’a ke fuskanta ba, hakan na iya haifar da rikici a nan gaba.

“Idan gwamnati ba ta saurari kokensu ba—musamman matasa da suka fusata—to nan gaba abubuwa ba za su yi kyau ba,” in ji shi.

“Waɗanda suka hana a samu sauyi cikin lumana, za su gamu da sauyi ta hanyar tashin hankali.”

Obasanjo ya ƙara da cewa idan shugabannin Afirka suka yi watsi da wannan gargaɗi, hakan na iya haddasa rikici a nahiyar gaba ɗaya.

“Yin watsi da wannan gargaɗi kamar yin rawa ne lokacin da gidanka ke ci da wuta,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gargadi Miyagun ƙwayoyi Najeriya Sarakunan Gargajiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kissoshin Rayuwa: Imam Al-Hassan 114

114-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissiso da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin dastane rastan, ko kum littafin mathnawi na maulana Jalaluddeen rumi. Ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu na yau.

///… Masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Al-hassan limami na biyu daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s), kuma da na farko ga Fatimah(s) diyar manzon All..(s), sannan jikansa na farko.

A cikin shirimmu da ya gabata, mun yi maganar yadda Khalifa Uthman ya wanye da Ammar dan Yasir ( R), mun ji yadda Ammar ya tashi da shi da iyayensa suka fara karban musulunci a Makka, da kuma yadda suka yi shahada a hannun Abu Jahal, sannan yadda Ammar ya kubuta daga sahrrinsa bayan ya fadi abinda suke so, ba da sonsa ba. Amma alkur’ani ya sauka yana tabbatar masa da Imani.

Sannan munji yadda manzon All…(s) yake himmantuwa da al-amarin Ammar don Yasir ba don iyayensa su ne shahidar na farko a makka ko a musulunci ba, sai har da cewa yana da Ikhlasi da kuma tsoron All… don haka manzon All..(s) yana girmama Ammar dan yasir ne saboda tsoron All…da kusancinsa da shi. Saboda a hadisan da aka karbo daga gareshi (s) dangane da Ammar suna maganane a kansa, kamar . Inda yake cewa. All..kayi fushi da wanda yayi fushi da Ammar. Sannan manzon All..yayi masu alkawali da shiga aljanna tun suna Makka, inda yake cewa: Ya ku yan gidan yasir kuyi hakuri laillai makomarku aljanna ce.

Sannan munji yadda ya narke a cikin son Aliyu dan Abitalib (a) bayan wafatin manzon All… Da kuma yadda Khalifa Uthman ya sa aka dakeshi har ya suma, har sau biyu.

A cikin shirimmu nay au zamu yi magana kan yadda aka yi wa Imam Alhassan (a), dangane da wai yana son Khalifa Uthman, kuma yana bakin ciki da kissansa, wanda Taha Hussain ya kawo a cikin littafinsa –Fitnatul Kubra.

Wasu malaman tarihi sun ruwaito hadisan kariya sun jinginawa Imam Alhassan dan Aliyu dan Abitalib (a) dangane da Khalifa Uthman, sun riya cewa Imam Alhassan (a), yana daga cikin masoyan khalifa Uthman, kuma yana sonshi har cikin zuciyarsa. A cikin rayuwarsa da kuma bayan kashe shi.

Dr Taha Hussain yana daga cikin wadanda suka tafi a kan wannan ra’ayin, inda yake fada cikin littafinsa Ftnatul Kubra, yana cewa” Hassan (a) bai gushe ba yana son Uthman, ya kasance masoyin Uthman ne da gaske, sai dai bai zare takobi don neman fansar jininsa ba, don bayan ganin hakan hakkinsa ne, wasu lokutan yakan wuce gona da sonsa Uthman har sai da a fadawa babansa (Imam Ali) abinsa dai dace ba. Kamar yadda, masu ruwaye sun ruwato daga Ali (a) ya wuce dansa Imam Hassan (a) yana alwala, sai ya ce masa, ka kyautata alwala, sai ya bashi wannan amsar mai daci, inda wai yana ce masa (hakika kun kashe wani mutum a jiya yana kyautata alwala). Sannan Aliyu (a) bai kara wani abu ba sai wannan Kalmar, (hakika All..ya tsawaita sonka ga Uthman).

Sai dai idan muka dubi wannan ruwayar wanda Taha Hussain ya kawo shi don karfafa ra’ayinsa, hakaka Balaziri ya ruwaitoshi, dada Mada’in, a cikin littafinsa ‘Al-ansabul Al-ashraaf JZ 5 sh 81, Shi wannan Mada’ini an sanshi da kin iyalan gidan manzon All..(a) , wato nasibi ne, sannan an sanshi da kirkiro hadisai na yabo da goyon baya ga banu umayya, yana jinginawa manzon All..(s).

Kuma manufarsa da kirkiro wannan hadisin ita ce tsarakaka banu Umayya, ta jikan manzon All..(s) mai tsari Imam Hassan (a). Don ya nuna cewa salihan bayi kamar Jikan manzon All..(s) yana son Uthman. Banda raunin sanadin wannan hadisin, ga wasu karin abin lura a cikinsa.

01- Idan har da gaskiya ne, Imam Ali (a) ya na son yi wa dansa gyara a alwalarsa, to me yasa Imam Hassan (a) zai fada masa wannan kalmomi masu daci?, Sannan A lokacinda aka kashe Khalifa Uthman, Imam Hassan (a) yana dan shekara 32 a duniya bai iya alwala ba? Imam Hassan (a) ya tashi a gaban manzon All..(s) yana dan shekara 7 a duniya, kakansa manzon All..(s) ya kaura daga wannan duniya, amma bai koyawa jikansa na farko, alwala ba?

Sai ya yana dan shekara fiye da 30 ne babazansa zai koya masa al-walah, ? ko way a san wannan ba haka yake ba.

Sannan ina hadisin nan da aka bayyana cewa Imam Hassan da Hussain (a) suka ga wani dattijo bai iya alwala ba, sai tunda su yara ne a lokacin sai suka yi dubara ta kyautata masa al-walansa, inda dayansu yayi alwala irin na dattijo sai dayan kuma yayi alwala mai kyau, sai dattajan ya gano cewa da shi ake nufi sai ya gyara alwalansa. ?

Wanda ya nuna cewa Imam AlHassan da Alhussain (a) suna koyawa mutane alwala tun kakansu manzon All..(s) ya na da ransa a duniya.

02-Sun ce Imam Alhassan (a) yana daga cikin masu kare khalifa Uthman a lokacinda yan tawaye suka yiwa gidansa kofar rago, kuma yana haka tare da Umurnin babansa Imam Ali(a) ne, to ta yaya a wannan hadisin Imam Hassan yana zargin babansa da kashe Uthman? .

Al-hali mun san cewa Imam Hassan yana tare da mahaifinsa, a yakin Jamal da kuma yakin siffin, a lokacinda yayi wadanda suke tuhumarsa da kashe Khalifa Uthman, suna cewa suna yakarsa ne don daukar fansar jinin Uthman. Imam Alhassan da Alhussain duk suna tare da mahaifinsu a wadannan wurare suna goyon bayansa, kuma basa tuhumarsa da kashe Khalifa Uthman.

Wannan ya tabbatar mana cewa, Mada’ini ya kirkiro wannan hadinsin ne tare da manufar da muka bayyana.

03-Ayyukan Uthman ne suka kasheshi, ya dorawa mutanen Masar da Kufa danginsa suka yi ta kashe su da kuma zaluntarsu, sun kawo kokari a Madina ya ki amsa korafe-korafensu, a lokacinda ya amsa kiran mutanen masar, daga baya ya warware.

A nan sai suka ce ko ya sauka daga khalifanci ko kuma su kasheshi, da yaki sauka suka kashe kashe. Imam Ali (a) bai da hannu ko kadan wajen kissan Khalifa Uthman, ta yaya dansa Imam Hassan (a), kamar yadda ya zo a cikin Hadisin Mada’ini,  zai tuhum- babansa da kissan Uthman, kamar yadda wannan hadisin yake cewa,  ya san cewa ba haka ne ba.?  

Amma abinda ya faru kafin kissan Khalifa na uku,  shi ne cewa, Khalifa Uthman ya aikata abubuwan da dama wadanda basu dace ba, har sai ya kai ga ba wani kare shi a cikin sahabban manzon All..(s) a Madina.

Hatta, talha da zubai da Abdurrahman bin Auf, wanda ya dorashi kan khalifancin, kuma  wadanda ya yi masu ni’imoni, masu yawa, sun dawo daga rakiyarsa.

Duk sun dawo suna fushi da shi. Ta yaya wadannan sahabban manzon All..(s) da salihan bayi daga cikinsu wadanda muka ambata a baya, kamar Abuzar, Ammar, Abdullahi dan Mas’ud da Aliyu dan Abi talib da sauransu duk suna aibata shi. Amma sai Imam Hassan (a) ya zama ya na sonsa?. Ba zai yu ba.

Don haka tare da wannan zamu ga cewa, ba kuma wata kima ga wannan Hadisin a sanadinsa da mataninsa. Abin mamaki shi ne, ta yaya Taha Hussain bai yi bincike mai zurfi a cikin wannan hadisin ba har ya zo ya fada cikin wannan tatsuniyar.

Don haka a lokacinda ayyukan Uthman suka zama abin tattaunawa a ko ina a Madina da sauran manya manyan garuruwan musulmi, sai zabubbu cikin sahabban manzon All..suka taro suka yi shawara, suka kuma yanke shawara kan cewa dole ne su sauya shugabancin musulmi. Don haka suka aika wasiku zuwa manya manyan kasashen musulmi suna neman taimakonsu da makamai da kuma sojoji.

Ga Nassin abinda ya zo cikin daya daga cikin wasikun da suka rubuta. Wannan wasikar zuwa ga mutanen Masar.

{Daga muhijiruna na farko, da sauran shura, zuwa ga wadanda suke kasar Masar, daga sahabbai da kuma masu binsu wato (tabi’ina), Bayan haka:

Da ku zo wajemmu, ku kawo dauki ga khalifancin manzon All..(s) kafin ma’abutanta, su kwaceta su kwaceta, to lalle lillafin All.. an sauya shi (ba’a aiki da shi),kuma sunnar manzon All..(s) an sauya ta, kuma hukunce, hukuncen khalifofi biyu an sauyasu, Muna hada All…kan cewa duk wanda ya karabta wannan takardan, daga cikin sahabban manzon All…(s)  da suka saura, da mabiyansu da kyautatawa, face ya taho mana, don ya karbo mana hakkimmu, kuma mu bashi hakkinsa, to ku zo mana idan har kunyi Imani da All..da ranar lahirah, (ku zo ku) ku tsaida gaskiyar bisa tafarki bayyananniya wanda manzonku (s) ya barku a kanta, kuma wacce khalifofi suka barku a kanta, an rinjayemu kan hakkimmu, an mamaye dukiyarmu, kuma an shiga tsakanimmu da al-amarimmu, kuma khalifanci bayan bayan bayan manzon All..(s) ta kasance khalifancin annabi, kuma mai rahama, amma a yau ta zama mulki na zalunci, wato wanda ya sami rinjaye ya ci.. …}.

Wannan kadan Kenan daga wasikar da sahabbai muhajirun suka rubutawa suran sahabban a wasu wurare, kuma Ibn Kutaiba ya kawo ta a cikin littafinsa Al-imama wassiya shafi na 35.

Sannan wadan wasikar ta ambaci abubuwa da dama wadanda suka fadawa daular musulunci da musulmi saboda mulkin Uthman.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Sama Da Masu Sayayya Daga Ketare 220,000 Ne Suka Halarci Bikin Baje Kolin Canton Karo Na 137
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Al-Hassan 114