Jajircewa Ce Sirrin Samun Daukakata A Masana’antar Kannywood -Sadik Sani Sadik
Published: 16th, March 2025 GMT
Abinda ya sa nike fatan ganin na zama gwamna shi ne saboda banida wani burin da ya wuce in ga cewar matsalar tsaro ta kau a Nijeriya musamman Arewacin kasar inda wasu ke wasa da rayukan al’umma saboda wata bukata ta kashin kansu, wasu tsiraru na amfani da rayukan mutane a matsayin kasuwanci ko kuma don neman daukaka ya kara da cewa.
A ci gaba da hirar Sadik ya amsa tambayar da aka yi mashi a kan fina-finan da yayi da kuma wadanda yake kallo a matsayin wanda yafi so a cikinsu, inda ya ce daga cikin fina-finan da ya fito wadanda kuma yafi so, akwai Mati Da Lado sai kuma wani fim mai suna Dan Marayan Zaki.
Abinda ya sa nafi son wadannan fina finai shi ne ba don komai ba sai don kawai su na daya daga cikin ayyukan da nafi wahala kuma na kara samun gogewa a wannan sana’a tawa, hakazalika su ne fina-finan da aka fara sanina dasu kuma aka fara sanin wanene Sadik Sani Sadik da kuma abinda zan iya yi idan aka dora mani kyamara.
Daga karshe Sadik ya bayyana sirrin samun daukakarshi a masana’antar Kannywood, da cewa ba komai bane ya sa ya samu daukaka illa addu’ar iyaye da kuma jajircewa saboda na dauki harkar fim a matsayin babbar sana’ar da na dogara da ita yanzu, kuma nike rufawa kaina asiri.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha
Daga Usman Muhammad Zaria
Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu, Dr. Builder Muhammad Uba, ya umarci a gaggawata gyaran bututun da suka hada tashar tacewa da samar da ruwa yankunan Dutsawa da Kantudu.
Wannan mataki ya biyo bayan matsalolin da ake yawan fuskanta sakamakon lalacewar wutar lantarki da na’urar janareto, wanda ke hana jama’a samun ruwa yadda ya kamata.
Yayin da yake bayyana jimaminsa bisa wannan lamari, Dr. Muhammad Uba ya basu tabbacin cewa In Shaa Allahu matsalar ta zo karshe.
A cewarsa, majalisar ta kudirin aniyar yin duk mai yiwuwa domin magance matsalolin da ake fuskanta tare da tabbatar da samun isasshen tsaftataccen ruwan sha ga al’umma.
Ya yi alkawarin tura dukkan kayan aiki da ake bukata domin ganin an warware matsalar.
Dr. Muhammad Uba ya kuma bukaci ma’aikatan hukumar ruwa ta Birnin Kudu da su kara jajircewa wajen kula da tsarin domin kauce wa sake fuskantar irin wannan matsala a gaba.
“Ina karfafa gwiwar dukkan ma’aikatan hukumar ruwa da su kasance masu lura, su zama masu saurin daukar mataki, kuma su kawar da duk wani cikas da zai hana cimma burin samar da ruwa mai dorewa a ko’ina cikin Birnin Kudu.”
Shugaban ya bayyana cewa aikin da ake yi a babbar tashar tacewa da samar da ruwan sha ya kusa kammaluwa.
A cewarsa, wannan aikin tare da gyaran bututun da ake yi yanzu na daga cikin babban shirin gwamnatinsa na inganta samar da ruwa a fadin karamar hukumar.
Wasu daga cikin mutanen yankin sun ce wannan mataki ya nuna jajircewar Dr. Uba wajen inganta muhimman ababen more rayuwa da kuma kyautata jin dadin al’ummar Birnin Kudu.