Aminiya:
2025-07-23@23:45:20 GMT

Tsohon Ministan Ilimi, Farfesa Jibril Aminu, ya rasu

Published: 5th, June 2025 GMT

Tsohon malamin makaranta, dan siyasa kuma ambasada, Farfesa Jibril Aminu ya rasu yana da shekara 85.

Wata majiya daga iyalan mamacin ta tabbatar da rasuwar, kuma Kwamishinan Gidaje da Raya Birane na jihar Adamawa, Hon Abdullahi Prambe ma ya tabbatar da haka.

Ya ce, “Ba za a taba mantawa da gudunmawar shi ba musamman a bangaren ilimi da kiwon lafiya da kuma shugabanci.

Wata majiya da ke da kusanci da mamacin ta ce za a yi jana’izarsa da misalin karfe 2:00 na rana a Masallacin Kasa da ke Abuja.

Sai dai kawo yanzu, iyalai da ’yan uwan mamaci bas u fid da cikakken bayani kan yadda za a yi jana’izar mamacin ba ko kuma musabbabin rasuwarsa.

An haifi Farfesa Jibril Aminu a garin Song na jihar ta Adamawa a shekara ta 1939, kuma ya rike mukamai da dama a Najeriya.

Daga cikin mukaman da ya rike akwai Ministan Ilimi da Ministan Man Fetur da Jakadan Najeriya a Amurka sannan ya taba zama Sanatan Adamawa ta Tsakiya.

Bugu da kari, Farfesa Jibril kwararren likitan zuciya ne da ya jima yana bayar da gudunmawa wajen ci gaban kasa a fannoni daban-daban.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farfesa Jibril

এছাড়াও পড়ুন:

An kaddamar Da Wani Shiri Na Ba ‘Yan Mata 200,000 Tallafin Audugar Mata A Kano

An shawarci mata da su daina amfani da tsumma ko soson katifa, da takarda a lokacin al’adar su don inganta tsafta da rigakafin matsalolin lafiya.

 

Jami’ar tallafawa masu kula da tsaftar jinin haila a jihar Kano (MH-NoW) Amina Sabiu Musa ta yi wannan kiran ne a lokacin wani taron karawa juna sani na tsaftar jinin haila ga kwararrun ‘yan jarida da masu fada a ji a shafukan sada zumunta da aka gudanar a Kano.

 

A cewarta, shirin na MH-NoW ya shafi ‘yan mata da mata masu shekaru 10 zuwa 24 su 200,000 da nufin magance matsalar talaucin kudin sayen audugar mata a fadin Najeriya.

 

Ta bayyana cewa shirin wanda Population Services International (PSI) Nigeria ta aiwatar, zai hada da masu raba kayan aikin tsaftar muhalli da za a sake amfani da su don taimakawa wajen rage radadin talauci a wannan banagen.

 

“Ana gudanar da aikin a wasu jahohin Najeriya, tare da mai da hankali kan dalibai da mata matasa a al’ummomi 15 dake fadin kananan hukumomin Ghari, Tsanyawa, da Nasarawa a Kano,” in ji Amina.

 

Shima da yake jawabi a wajen taron, mataimakin daraktan bincike da kididdiga na ma’aikatar mata, yara da masu bukata ta musamman ta jihar Kano, Alhaji Zubair Abdulmumin Zubair ya bukaci iyaye da su ba da fifiko ga tsaftar jinin haila ta hanyar samar da kayan tsafta da kuma jagoranci mai kyau ga ‘ya’yansu mata.

 

Ya nuna damuwarsa kan rahotannin da ke cewa dalibai mata da yawa ba sa zuwa makaranta a lokutansu sakamakon rashin samun kayayyakin tsaftar muhalli da kuma rashin audugar mata a lokacin al’ada.

 

Ya yi kira ga maza, iyaye, maza da mata da duk masu ruwa da tsaki da su yi watsi da tatsuniyoyi masu cutarwa game da jinin haila tare da tallafawa ilimin haila.

 

“Dole ne kuma a ilmantar da maza game da jinin haila don su fahimci sauyin yanayi da yanayin da mata ke fuskanta a lokacin al’ada,”

 

Wasu daga cikin mahalarta taron da suka zanta da gidan rediyon Najeriya Aminu Abdullahi da Hannatu Sulaiman Abba da kuma Maimuna O. Yusuf sun bayyana taron da ya dace.

 

A matsayinsu na masu yada labarai, sun yi alkawarin ba da horo ga wasu kuma za su yi amfani da dandamali daban-daban na don Magana akan haila.

 

 

Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa taron bitar ya samu halartar dimbin mahalarta.

 

Khadija Aliyu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Iraki Ta Yi Watsi Da Bukatar Amurka Akan Dakarun Sa Kai Na” Hashdus-sha’abi”
  • Matasa 3 sun rasu yayin wanka a rafi a Bauchi
  • UNICEF Ya Bukaci Jihar Kano Ta Bai Wa Yara Muhimmanci A Kasafin Kudi
  • Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai
  • Shugaban Amurka Trump Ya Bukaci Gurfanar Da Tsohon Shugaban Amurka Barack Obama A gaban Kuliya
  • Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
  • NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa
  • Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • An kaddamar Da Wani Shiri Na Ba ‘Yan Mata 200,000 Tallafin Audugar Mata A Kano
  • Wata Kungiyar Ta Bukaci Shugaban Kasa Ya Cika Alkwarin Marigayi Shugaba Buhari Game Da Shehu Usman Aliyu Shagari