Saudiya Ta Samar Da Wata Manhaja Ta Kiwon Lafiyar Mahajjata A Cikin Harsun 8 A Duniya
Published: 16th, May 2025 GMT
Ma’aikatar kiwon lafiya a kasar Saudia ta kaddamarda wata manhaja don kula da lafiyan mahajjata a hajjin bana, wanda aka tarjamata zuwa harsuna 8 a duniya.
Shafin yanar gizo na labarai Arabnews ya nakalto kamfanin dillancin labaran Saudi Press Agency (SPA) na fadar haka a yau Jumma’a. Ya kuma kara da cewa harsunan da ake samun manhajar a ciki suna hada da Arabiyya, Inglishi, Faransaci, Urdu, Farisanci, Indonesia, Malay da kuma Turkanci.
Manufar wannan manhajar ita ce bada shawara ga mahajjata kan yadda zasu kula da lafiyarsu a cikin wannan lokacinda Hajji na bana, wanda yake zuwa tare da zafi sosai.
Da farko manhajan ya bukaci mahajjata su yi amfani da laima don rage zafin da ke fadawa a kansu. Sannan su tabbatar da cewa sun yi alluran riga kifan da yakamata su yi tun suna kasashensu, wadanda suka hada da cutar Corona ko covid 19, shan inna, cutar shawara, da malariya, da sauransu. Wannan ya danganci daga kasar da mutum ya fito. Ana samun manhajan a yanar gizo ko a kan wayoyi da sauransu a kan adireshin
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya
Jakadan Pakistan a kasar Sin, Khalil Rahman Hashimi ya ce, “sabuwar dokar ta bayar da karin kariya har ma da wani sauki na musamman ga kamfanoni masu zaman kansu a kasar Sin. Akwai tanade-tanade da dama a kasar Sin wadanda suke bayar da kwarin gwiwa ga kamfanoni masu zaman kansu don su iya bunkasa harkokinsu da kuma ba da gagarumar gudummawa ga tattalin arzikin kasar Sin. Akwai samun moriya da dama da kuma goyon bayan gwamnati har ma da ba da kariya ta fuskar shari’a ga kamfanoni masu zaman kansu.”
Shi ma jakadan Nepal a kasar Sin, Krishma Prasad Oli ya ce, “dokar ta sahale wa kamfanoni su gudanar da ayyukansu ba tare da wani matsi ba. Akwai babbar dama da aka samu a halin yanzu saboda akwai takamaimiyar doka da ta bayar da damar shigar kamfanonin kasashen ketare cikin hadin gwiwa da kamfanonin kasar Sin kuma suna iya yin aiki tare.”
Tuni dai aka fara ganin alherin sabuwar dokar bisa yadda ’yan kasashen waje ke tururuwar kafa kamfanoni da harkokinsu na kasuwanci a kasar ta Sin. Sakamakon amanna da kafuwar dokar da kuma fara aikinta, an kafa kamfanoni da ’yan kasuwa na kasashen waje suka zuba jarinsu fiye da 24,000 a cikin watanni biyar na bana kamar yadda ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ta tabbatar a ’yan kwanakin nan. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp