Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Imanin Iran Da Tattaunawan Zaman Lafiya Amma Ba Za Ta Amince Da Barazana Ba
Published: 16th, May 2025 GMT
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Sun yi imani da tattaunawa da zaman lafiya ba tare da mika wuya ga barazana ba
A yayin ganawarsa da masu fafutukar siyasa da zamantakewa a lardin Kermanshah da ke yammacin kasar Iran a jiya Alhamis, shugaban na Iran Masoud Perzeshkiyon ya ce za a gudanar da shawarwari kan shirin makamashin nukiliyar Iran cikin karfin gwiwa da mutunta juna, yana mai jaddada wajabcin rashin mika wuya ko mika kai ga duk wata barazana.
Shugaba Pezeshkiyon ya jaddada cewa yin shawarwari ɗaya ne daga cikin ka’idodin hankali da zurfin tunani, amma ba a kan kowane farashi ba. Dole ne a gudanar da shawarwari cikin aminci da mutuntawa tare da bin ka’idojin kasa da kare kima. Iran ta yi imani da tattaunawa da zaman lafiya, amma ba za ta taba mika wuya ga barazana da umarni ba.
Sugaban kasar ya kara da cewa: Ci gaba da kuma cimma manyan buruka na bukatar azama, karfin gwiwa, da kuma sauya yanayin tafiyar da harkokin gudanarwa. Idan wani ya yi niyya don ya cimma manufa amma ya yi kasa a gwiwa a farkon mataki, to ba zai taba cimma burinsa ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran: Duk Wani Sabon Hari, Zai Fushin Sojojin Kasar
Wani babba`ani babba`sojojin kasar Iran ya gargadi HKI da kuma Amurka kan cewa duk wasu hare-hare kan kasar zai kara fushin sojojin kasar.
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto babban kwamandan sojojin sama na JMI Major General Abdolrahim Mousavi yana fadar haka a lokacin ganawarsa da babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Afrika ta kudu General Rudzani Maphwanya a yau talata a nan Tehran.
Janar Mousavi ya kara da cewa dakarun kare juyin juta halin musulunci a nan Iaran wato IRGC sune sojojin da suka fi kawo fada da yan ta’adda a duniya, sannan rundunar a shirye take ta yi aiki da sojojin Afrika Ta Kudu don samun irin kwarewan da rundunar take da shi a wannan bangaren a kuma sauran bangarori.
Ya kuma kara da cewa duniya taga yadda dakarun na IRGC suka maida martani kan HKI da kuma Amurka a yakin da suka dorawa kasar a kwanaki 12 a cikin watan yunin da ya gabata.
A wani bangaren babban kwamandan sojojin sama na dakarun IRGC ya bayyana cewa kasashen yamma musamman Amurka da HKI ba sa da alkawali, don haka zasu iya karya alkawalin da suka dauka da kowa a ko yauce idan sunga zasu sami biyar bukata.
Daga karshe Mousavi ya yabawa kasar Afirka ta kudu da gabatar da HKI a gaban kotun ICC saboda ayyukan kissan kare dangi da take aikatawa a Gaza.
A nashi bangaren Janar Maphwanya y ace, dangantaka tsakanin Iran da afirka ta kudu ya samo asali daga goyon bayan da JMI ta bawa gwagwarmayan mutanen kasar don samun yencinsu daga gwamnatin wariyar launin fata. Ya daga nan ne kasashen biyu suka aiki da juna a banari da dama daga ciki har da bangaren tsaro.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Larijani: Iraki Bata Daukan Umarni Daga JMI August 12, 2025 Iran Tace Ma’aikatar Harkokin Waje Kasarce Take Kula Da Lamuran Makamacin Nukliyar Kasar August 12, 2025 Armenia Ta Tabbatarwa Iran Zata Kula Da Muradunta Bayan Yarjeniya Da Azarbaijan A Amurka August 12, 2025 Araqchi: Babban Abin Kunya Ne Shuru Gwamnatocin Yammacin Turai Kan Abin Da Ke Faruwa A Gaza August 12, 2025 Larijani Ya Ce: ‘Yan Gwagwarmaya Sun San Abubuwan Da Suka Dace August 12, 2025 Iraki Ya Bukaci Tattaunawa Tsakanin Larabawan Yankin Tekun Farisa Da Iraki Da Iran August 12, 2025 Italiya Ta Janye Jirgin Ruwanta Daga Taken Bahar Maliya Saboda Barazanar ‘Yan Gwagwarmayar Yemen August 12, 2025 Majalisar Dinkin Duniya Ta Sanar Da Mutuwan Mutane 60 Saboda Yunwa A El-Fasher Na Sudan August 12, 2025 Iran da Iraki sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro August 12, 2025 Masar ta yi gargadin daukar tsauraran matakai domin kare muradunta August 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci