Aminiya:
2025-06-14@22:11:29 GMT

Mayaƙan ISWAP sun tarwatsa gada a Yobe

Published: 20th, April 2025 GMT

’Yan ta’addar ISWAP sun tarwatsa wata gada da ta haɗa garin Ngirbuwa da garin Goneri a Ƙaramar Hukumar Gujiba da ke Jihar Yobe.

Wannan na zuwa ne ƙasa da mako guda da ‘yan ta’addan suka lalata gadar nan ta Mandafuna da ta haɗa garin Biu da Damboa a Jihar Borno.

JAMB ta sauya ranar soma jarrabawar bana Manyan jami’an gwamnati sun halarci auren ’yar tsohon Gwamnan Bauchi

Majiyar leƙen asiri ta shaida wa Zagazola Makama cewa harin ya afku ne da misalin ƙarfe 10:30 na daren ranar ranar Alhamis ɗin da ta gabata, ta hanyar amfani da wani bam wajen lalata sauran sassan gadar.

Wannan aikin ta’addanci ya kawo cikas ga zirga-zirga tsakanin al’ummomin biyu da ma sauran al’ummomin yankin, lura da cewar gadar na kan hanyar Katarko ne zuwa garin Goneri.

Masana tsaro na nuna cewar, lalata wannan gadar mota na iya kawo cikas ga harkokin tsaro a wannan yanki, lura da cewar yankin na da iyaka da wasu dazuzzukan da ke da iyaka da dajin Sambisa da ya zama maɓoyar ‘yan ta’addan a wasu ɓangarorin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ISWAP Jihar Yobe

এছাড়াও পড়ুন:

An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe

A yayin da ake tsaka da bikin Ranar Dimokradiyya a Najeriya, al’ummar jihar Gombe sun wayi gari da sabuwar dokar takaita zirga-zirgar babura daga ƙarfe 7:00 na yamma zuwa ƙarfe 6:00 na safe a duk faɗin jihar.

Sanarwar da ta fito ne daga hannun Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ’Yan Sanda ta jihar, DSP Buhari Abdullahi, ranar Alhamis, a madadin kwamishinan ’yan sandan jihar Bello Yahaya.

Sanarwar ta ce an kafa dokar ne don rage ayyukan ta’addanci a fadin jihar.

Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato 

Kafa dokar na zuwa ne kwana uku bayan wasu matasa da ba a tantance su wane ne ba suka kashe wani magidanci mai suna Ahmad Aliyu, wanda aka fi sani da Amadi Kasiran, a unguwar Hammadu Kafi da ke Gombe, a daren Lahadi.

Sanarwar ta ƙara da cewa duk wanda aka kama ya karya dokar zai fuskanci hukunci mai tsauri, ciki har da gurfanar da shi a gaban kotu.

Kazalika, sanarwar ta ce dokar ta haramta ɗaukar mutum fiye da ɗaya a kan babur domin rage matsalar rashin tsaro a jihar.

“Dokar hana hawa babur da goyon biyu ta fara aiki ne daga yau, Alhamis, ranar bikin Dimokradiyya, har sai wani lokaci da ba a kayyade ba,” in ji Kakakin ’yan sandan.

Rundunar ’yan sandan ta ce an ɗauki wannan mataki ne don magance matsalar bata-gari na ‘’yan kalare’ da sauran ayyukan ta’addanci.

A lokacin da wakilinmu ya kai ziyara kwaryar birnin Gombe, filin wasa na Pantami ya kasance a rufe ba tare da alamar wani biki ba.

Sai dai ya gane wa idanunsa cewa an jibge jami’an tsaro a sassa daban-daban, ciki har da ’yan sanda, jami’an tsaro na farin kaya (DSS), da kuma ’yan banga.

Wannan sabuwar doka ta ja hankalin mutane da dama a jihar, musamman mazauna yankunan da aka fi samun matsalar tsaro.

Sai dai wasu na gani za ta kara jefa jihar cikin kuncin talauci sakamakon rufe shaguna da kasuwanni da wuri saboda rashin abun hawa wanda dama can baburan aka fi hawa saboda tsadar rayuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su
  • Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwaman Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa
  • An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe
  • Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • NAJERIYA A YAU: 12 Ga Yuni: Me Ranar Dimokuraɗiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya?
  • NAJERIYA A YAU: June 12: Me Ranar Demokradiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya?