Aminiya:
2025-05-21@20:38:50 GMT

Barcelona da PSG sun tsallaka zagayen kusa da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai

Published: 16th, April 2025 GMT

Paris St Germain ta kai zagayen daf da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai duk da rashin nasara da ta yi a hannun Aston Villa ranar Talata a Villa Park.

Aston Villa ta yi nasarar cin PSG 3-2, inda Tielemans da McGinn da kuma Konsa suka ci mata ƙwallayen a wasa falle na biyu a zagayen kwata fainal.

DAGA LARABA: Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan Riƙo Ana barazanar korar sojojin Isra’ila da ke neman a kawo ƙarshen yaƙin Gaza

Ita kuwa ƙungiyar ta Faransa ta ci nata ƙwallayen ta hannun Hakimi da kuma Nuno Mendes.

PSG ta kai zagayen gaba da cin 5-4 gida da waje jimilla, bayan da ta yi nasarar cin 3-1 a makon jiya a Faransa.

Ita ma Barcelona da ke buga gasar La Liga ta kai matakin daf da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai ta bana duk da shan kashi da ta yi a hannun Borussia Dortmund.

Dortmund dai ta taka wa Barcelona burki, bayan wasa 24 a jere ba tare da rashin nasara ba a dukkan kaka a bana.

Ƙungiyar ta Jamus ta doke ta Sifaniya da 3-1 a wasa falle na biyu na Gasar Zakarun Turai zagayen kwata fainal da suka fafata a Jamus ranar Talata.

Duk da haka Barcelona ta kai zagayen daf da ƙarshe sakamakon cin 5-3 gida da waje jimilla, bayan da ta ci 4-0 a makon jiya a Sifaniya.

Serhou Guirassy ne ya ci wa Dortmund ƙwallo uku rigis, wanda ta farko a bugun fenariti, sannan ya ƙara biyu bayan an dawo hutun rabin lokaci.

Barcelona ta zare ɗaya ne ta hannun Ramy Bensebaini, ɗan wasan Dortmund da ya ci gida.

Rabon da Barcelona ta yi rashin nasara tun cikin Disamba, bayan da Atletico Madrid ta ci ta 2-1, daga nan ta yi karawa 24 a jere ba tare da rashin nasara ba har da canjaras huɗu daga ciki.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Barcelona Borrusia Dortmund Gasar Zakarun Turai a Gasar Zakarun Turai rashin nasara

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo

Ya misalta rashin basaraken da cewa, ba rashin ne kawai ga iyalai ko al’ummar masarautarsa ba, a’a rashi ne ga illahirin masarautar Bauchi da ma jihar Bauchi baki ɗaya.

 

Gwamna Muhammad ya misalta Alhaji Garba a matsayin babban basaraken gargajiya wanda aka sani da hikima, tawali’u, da sadaukar da kai ga hidimta wa al’ummarsa.

 

“Ya kasance mutum mai dattako wanda ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen kyautata zaman lafiya da cigaba,” in ji gwamna Bala.

 

Gwamnan sai ya yi addu’ar Allah ya jiƙan mamacin ya gafarta masa kura-kuransa tare da sanya shi cikin aljanna maɗaukakiya. Ya kuma jajanta wa masarautar Bauchi, iyalai da al’ummar jihar da fatan Allah ba su haƙurin juriya na wannan babban rashin..

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashin Tsaro: Matasa Sun Yi Zanga-zangar Toshe Babbar Hanya Saboda Satar Mutane A Edo
  • Sakataren Harkokin Wajen Amurka Ya Ce; Gwamnatin Siriya Zata Iya Rugujewa Cikin ‘Yan Makonni
  • EU ta dage takunkumin da ta kakaba wa Syria
  • Gwamnati za ta sayar da gidaje 753 da EFCC ta ƙwato a hannun Emefiele 
  • Fransa Ta Kira Yi Kasashen Turai Da Sake Bitar Alakarsu Da “Isra’ila”
  • Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo
  • Shugaba Kasar Lebanon Ya Ce Kungiyar Hizbullah Bata Da Zabi Sai Abinda Gwamnati Ta fada
  • Gasar Wasanni Ta Kasa: FCT Ta Lallasa Borno Da Ci 4-1 A Wasan Farko
  • Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto
  • CAN U20 : Afirka ta Kudu ta lashe kofi na farko