Aminiya:
2025-04-30@22:56:34 GMT

Barcelona da PSG sun tsallaka zagayen kusa da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai

Published: 16th, April 2025 GMT

Paris St Germain ta kai zagayen daf da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai duk da rashin nasara da ta yi a hannun Aston Villa ranar Talata a Villa Park.

Aston Villa ta yi nasarar cin PSG 3-2, inda Tielemans da McGinn da kuma Konsa suka ci mata ƙwallayen a wasa falle na biyu a zagayen kwata fainal.

DAGA LARABA: Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan Riƙo Ana barazanar korar sojojin Isra’ila da ke neman a kawo ƙarshen yaƙin Gaza

Ita kuwa ƙungiyar ta Faransa ta ci nata ƙwallayen ta hannun Hakimi da kuma Nuno Mendes.

PSG ta kai zagayen gaba da cin 5-4 gida da waje jimilla, bayan da ta yi nasarar cin 3-1 a makon jiya a Faransa.

Ita ma Barcelona da ke buga gasar La Liga ta kai matakin daf da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai ta bana duk da shan kashi da ta yi a hannun Borussia Dortmund.

Dortmund dai ta taka wa Barcelona burki, bayan wasa 24 a jere ba tare da rashin nasara ba a dukkan kaka a bana.

Ƙungiyar ta Jamus ta doke ta Sifaniya da 3-1 a wasa falle na biyu na Gasar Zakarun Turai zagayen kwata fainal da suka fafata a Jamus ranar Talata.

Duk da haka Barcelona ta kai zagayen daf da ƙarshe sakamakon cin 5-3 gida da waje jimilla, bayan da ta ci 4-0 a makon jiya a Sifaniya.

Serhou Guirassy ne ya ci wa Dortmund ƙwallo uku rigis, wanda ta farko a bugun fenariti, sannan ya ƙara biyu bayan an dawo hutun rabin lokaci.

Barcelona ta zare ɗaya ne ta hannun Ramy Bensebaini, ɗan wasan Dortmund da ya ci gida.

Rabon da Barcelona ta yi rashin nasara tun cikin Disamba, bayan da Atletico Madrid ta ci ta 2-1, daga nan ta yi karawa 24 a jere ba tare da rashin nasara ba har da canjaras huɗu daga ciki.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Barcelona Borrusia Dortmund Gasar Zakarun Turai a Gasar Zakarun Turai rashin nasara

এছাড়াও পড়ুন:

Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 

“Gwamnati ta amince da hada hannu da shugabannin al’umma na cikin gida domin tabbatar da tsaro.

 

“Muna gode muku kan abin da kuke yi. Amma muna bukatar Sarakuna su yi magana da mutanenmu kan kokarin da dukkanmu muke yi don kare al’ummominmu daga masu kutse.”

 

Gwamnan ya yi kira da a inganta hadin gwiwa a tsakanin al’umma da hukumomin tsaro domin kare rayuka da dukiyoyi.

 

Mataimakin Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Kwara, Alhaji Ibrahim Bologi II, wanda shi ne Etsu Patigi, ya yaba wa gwamnan bisa hada gwiwa da su domin tabbatar da tsaro a jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027
  • Yadda ta kaya a wasannin kusa da na ƙarshe na Gasar Zakarun Turai
  • Riza’i: Babu Hannun  Waje A Cikin Hatsarin Da Ya Faru A Tashar Ruwa Ta Shahid Raja’i
  • Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku