Barcelona da PSG sun tsallaka zagayen kusa da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai
Published: 16th, April 2025 GMT
Paris St Germain ta kai zagayen daf da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai duk da rashin nasara da ta yi a hannun Aston Villa ranar Talata a Villa Park.
Aston Villa ta yi nasarar cin PSG 3-2, inda Tielemans da McGinn da kuma Konsa suka ci mata ƙwallayen a wasa falle na biyu a zagayen kwata fainal.
DAGA LARABA: Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan Riƙo Ana barazanar korar sojojin Isra’ila da ke neman a kawo ƙarshen yaƙin GazaIta kuwa ƙungiyar ta Faransa ta ci nata ƙwallayen ta hannun Hakimi da kuma Nuno Mendes.
PSG ta kai zagayen gaba da cin 5-4 gida da waje jimilla, bayan da ta yi nasarar cin 3-1 a makon jiya a Faransa.
Ita ma Barcelona da ke buga gasar La Liga ta kai matakin daf da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai ta bana duk da shan kashi da ta yi a hannun Borussia Dortmund.
Dortmund dai ta taka wa Barcelona burki, bayan wasa 24 a jere ba tare da rashin nasara ba a dukkan kaka a bana.
Ƙungiyar ta Jamus ta doke ta Sifaniya da 3-1 a wasa falle na biyu na Gasar Zakarun Turai zagayen kwata fainal da suka fafata a Jamus ranar Talata.
Duk da haka Barcelona ta kai zagayen daf da ƙarshe sakamakon cin 5-3 gida da waje jimilla, bayan da ta ci 4-0 a makon jiya a Sifaniya.
Serhou Guirassy ne ya ci wa Dortmund ƙwallo uku rigis, wanda ta farko a bugun fenariti, sannan ya ƙara biyu bayan an dawo hutun rabin lokaci.
Barcelona ta zare ɗaya ne ta hannun Ramy Bensebaini, ɗan wasan Dortmund da ya ci gida.
Rabon da Barcelona ta yi rashin nasara tun cikin Disamba, bayan da Atletico Madrid ta ci ta 2-1, daga nan ta yi karawa 24 a jere ba tare da rashin nasara ba har da canjaras huɗu daga ciki.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barcelona Borrusia Dortmund Gasar Zakarun Turai a Gasar Zakarun Turai rashin nasara
এছাড়াও পড়ুন:
Sudan Ta Zargi Janar Haftar Na Libiya Da Goyon Bayan ‘Yan Tawayen Kasarta Na Rapid Support Forces
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sudan na zargin Janar Haftar na Libiya da goyon bayan hare-haren ‘yan tawayen kasarta
Sojojin Sudan da ma’aikatar harkokin wajen Sudan sun zargi Janar Khalifa Haftar mai ritaya da goyon bayan hare-haren da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces suka kaddamar a kan iyakokin Sudan da Masar da Libya.
A cewar sanarwar da Rundunar Sojin Sudan ta fitar, Dakarun Kai Daukin Gaggawa na Rapid Support Forces da ke samun goyon bayan Bataliyar Salafiyya ta Haftar, sun kai hare-hare kan iyakokin Sudan da Masar da Libya, da nufin kwace wadannan yankuna masu matukar muhimmanci.
Sanarwar ta kara da cewa: Wannan shiga tsakani da dakarun Haftar suka yi kai tsaye ya zama “cin zarafi a fili” ga ‘yancin Sudan da al’ummarta, tare da nuna cewa harin wani bangare ne na makircin kasa da kasa da na yanki bisa cikakkiyar masaniya da fahimtar kasashen duniya.
Sojojin kasar ta Sudan sun jaddada aniyarsu ta tunkarar wannan ta’addanci, ba tare da la’akari da irin makircin da ake kullawa ba, gami da tabbatar da aniyarsu ta kare ‘yancin kan kasa tare da goyon bayan al’ummar Sudan.